Aminiya:
2025-07-27@13:17:25 GMT

LP za ta ceto Nijeriya daga halin da APC ta jefa ta — Nenadi Usman

Published: 27th, July 2025 GMT

Shugabar riƙo ta jam’iyyar Labour (LP) ta ƙasa, Sanata Nenadi Usman, ta ce jam’iyyarsu ta shirya tsaf domin gyara manyan kura-kurai da gazawar da gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki ta jefa Nijeriya a ciki.

Sanata Usman ta bayyana hakan ne a wata ganawa da manema labarai a ƙarshen mako a Jihar Kaduna dangane da abinda da ke faruwa a cikin jam’iyyar LP.

Rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara 650 a Katsina — MSF Za mu ba da damar shigar da kayan agaji a Gaza — Isra’ila

Sanatar ta buƙaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da goya musu baya domin a cewarta, jam’iyyar LP ce za ta farfaɗo da fatan da al’umma ke da shi da kuma ɗaga martabar ƙasar nan.

A cewarta, “Gwamnatin APC ta fi kowacce gwamnati a tarihin kasar nan jefa talakawan Nijeriya cikin ƙuncin rayuwa da fatara.”

Dangane da sauya sheƙa da ‘yan siyasa ke yi daga jam’iyyun adawa zuwa jam’iyyar APC mai mulki, ciki har da wasu daga cikin ‘yan LP, Sanata Usman ta bayyana hakan a matsayin abin takaici, inda ta bayyana shi a matsayin abin kunya ne mutum ya samu nasara a cikin wata jam’iyya sannan ya canza sheƙa zuwa wata jam’iyyar.

Sai dai ta ce jam’iyyar LP ba ta damu da waɗannan sauya sheƙar ba, matuqar jama’ar ƙasa na tare da ita.

“Karfinmu yana fitowa ne daga goyon bayan talakawan Nijeriya, ba daga mahandama masu son kansu ba.”

Sanata Usman ta yarda cewa jam’iyyar ta aikata kura-kurai, musamman wajen tsayar da ‘yan takarar da ba su da cikakken fahimta ko biyayya ga manufofin jam’iyyar, amma ta tabbatar da cewa irin wannan kuskure ba zai maimaitu ba a nan gaba.

“Da yawa daga cikin waɗanda suka fice daga jam’iyyar tun farko ba su da cikakkiyar fahimta kan akidar gina sabuwar Nijeriya.

“Ficewarsu tana ƙara mana ƙwarin gwiwa kuma hakan yana fayyace mana masu kishin jam’iyyar na gaskiya,” inji ta.

Ta kuma buƙaci dukkan ‘ya’yan jam’iyyar da ke da saɓani da su rungumi sulhu su haɗa kansu yayin da jam’iyyar ke shirin ƙaddamar da sabunta rajistar mambobinta, gudanar da tarukan gunduma da na jihohi, da kuma babban taron ƙasa wanda tuni an samu amincewa daga Kwamitin Zartaswa na Kasa (NEC).

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Ya ce tituna a Arewa sun lalace kuma gwamnati tana nuna rashin kulawa ga yankin. “Jiya da jirgi zan biyo na taho, amma aka ɗage jirgi daga ƙarfe 3 na yamma zuwa 8 na dare, sai na taho ta mota. Daga Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano abin takaici ne. Wannan aikin titi tun lokacin farkon hawa gwamnatin APC ake yinsa.”

Kwankwaso ya kara da cewa ana gudanar da manyan ayyuka a Kudu cikin hanzari, amma an bar ayyuka masu mahimmanci a Arewa babu kulawa.

“Muna jin ana gina titi daga Kudu zuwa Gabas. Muna maraba da ci gaba a ko’ina a Nijeriya. Amma gwamnati tana ɗaukar duk arzikin ƙasa ta zuba a ɓangare ɗaya kaɗai, ba ta yin aiki da ra’ayin ‘yan ƙasa gaba ɗaya,” cewarKwankwaso.

Ya roƙi gwamnatin Tinubu da ta sake duba tsarin rabon arziki tare da tabbatar da yin adalci a dukkan yankuna.

“Lokaci ya yi da gwamnati za ta sauya, ta tabbatar wa da ’yan Nijeriya cewa gwamnati ce ta ƙasa gaba ɗaya, ba ta wani ɓangare kawai ba,” in ji Kwankwaso.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu
  • Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu
  • Super Falcons ta lashe gasar WAFCON karo na 10 bayan doke Maroko
  • Super Falcons sun lashe gasar WAFCON karo na 10 bayan doke Maroko
  • HOTUNA: Yadda Kwankwaso ya karɓi ’yan APC zuwa NNPP a Kano
  • Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
  • Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato
  • An rantsar da Nentawe sabon shugaban APC na ƙasa
  • Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa