LP za ta ceto Nijeriya daga halin da APC ta jefa ta — Nenadi Usman
Published: 27th, July 2025 GMT
Shugabar riƙo ta jam’iyyar Labour (LP) ta ƙasa, Sanata Nenadi Usman, ta ce jam’iyyarsu ta shirya tsaf domin gyara manyan kura-kurai da gazawar da gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki ta jefa Nijeriya a ciki.
Sanata Usman ta bayyana hakan ne a wata ganawa da manema labarai a ƙarshen mako a Jihar Kaduna dangane da abinda da ke faruwa a cikin jam’iyyar LP.
Sanatar ta buƙaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da goya musu baya domin a cewarta, jam’iyyar LP ce za ta farfaɗo da fatan da al’umma ke da shi da kuma ɗaga martabar ƙasar nan.
A cewarta, “Gwamnatin APC ta fi kowacce gwamnati a tarihin kasar nan jefa talakawan Nijeriya cikin ƙuncin rayuwa da fatara.”
Dangane da sauya sheƙa da ‘yan siyasa ke yi daga jam’iyyun adawa zuwa jam’iyyar APC mai mulki, ciki har da wasu daga cikin ‘yan LP, Sanata Usman ta bayyana hakan a matsayin abin takaici, inda ta bayyana shi a matsayin abin kunya ne mutum ya samu nasara a cikin wata jam’iyya sannan ya canza sheƙa zuwa wata jam’iyyar.
Sai dai ta ce jam’iyyar LP ba ta damu da waɗannan sauya sheƙar ba, matuqar jama’ar ƙasa na tare da ita.
“Karfinmu yana fitowa ne daga goyon bayan talakawan Nijeriya, ba daga mahandama masu son kansu ba.”
Sanata Usman ta yarda cewa jam’iyyar ta aikata kura-kurai, musamman wajen tsayar da ‘yan takarar da ba su da cikakken fahimta ko biyayya ga manufofin jam’iyyar, amma ta tabbatar da cewa irin wannan kuskure ba zai maimaitu ba a nan gaba.
“Da yawa daga cikin waɗanda suka fice daga jam’iyyar tun farko ba su da cikakkiyar fahimta kan akidar gina sabuwar Nijeriya.
“Ficewarsu tana ƙara mana ƙwarin gwiwa kuma hakan yana fayyace mana masu kishin jam’iyyar na gaskiya,” inji ta.
Ta kuma buƙaci dukkan ‘ya’yan jam’iyyar da ke da saɓani da su rungumi sulhu su haɗa kansu yayin da jam’iyyar ke shirin ƙaddamar da sabunta rajistar mambobinta, gudanar da tarukan gunduma da na jihohi, da kuma babban taron ƙasa wanda tuni an samu amincewa daga Kwamitin Zartaswa na Kasa (NEC).
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin
Kasashen Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan hadin kan Musulmi game da halin da ake ci a yankin
Wannan bayannin ya fito ne a yayin ganawar sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Ali Larijani da yarima mai jiran gado na kasar Saudiyya Mohammed bin Salman a birnin Riyadh inda suka tattauna kan dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da kuma halin da ake ciki a yankin.
Ganawar dai ta nuna wani muhimmin mataki a huldar diflomasiyya ta tsakanin Tehran da Riyadh.
Larijani ya tafi Saudiyya ne bisa gayyatar da ministan tsaron kasar ya yi masa, inda ya jagoranci tawagar da ta hada da mataimakin sakataren harkokin kasa da kasa Ali Bagheri Kani da mai ba da shawara kan harkokin yankin Gulf na Farisa Mohammad Ali Bek.
Ganawar na zuwa ne kwana guda kacal bayan da shugaba Masoud Pezeshkian ya gana da bin Salman a gefen taron gaggawa na kasashen Larabawa da Musulunci da aka yi a birnin Doha, inda bangarorin biyu suka nuna gamsuwarsu da yadda huldar dake tsakanin kasashen biyu ke kara habaka.
Ziyarar Larijani a Riyadh ita ce ziyararsa ta uku a yankin tun bayan hawansa mulki a ranar 5 ga watan Agusta, biyo bayan ziyarar da ya kai a Iraki da Lebanon.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci