Aminiya:
2025-07-26@23:16:45 GMT

Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCN

Published: 26th, July 2025 GMT

Wasu yankuna a Jihar Legas, na iya fuskantar rashin wuta na tsawon kwanaki 25, yayin da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN), zai fara gyaran layin lantarkin Omotosho zuwa Ikeja ta Yamma mai ƙarfin 330kV.

A cewar sanarwar da kamfanin ya fitar a ranar Juma’a, 25 ga watan Yuli, aikin zai gudana kowace rana daga ƙarfe 8 na safe zuwa 5 na yamma, kuma za a kammala aikin a ranar Alhamis, 21 ga watan Agustan 2025.

Wani mutum ya buɗe Ofishin Jakadancin Indiya na bogi a ƙasar Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji

Kamfanin, ya bayyana cewa gyaran zai shafi raba wutar lantarki a wasu wurare, kuma hakan na iya janyo ɗaukewar wuta.

Sanarwar ta ce: “Abokan hulɗarmu za su iya fuskantar yawan ɗaukewa da ƙarancin wuta a wasu lokuta saboda aikin gyaran da za a yi.”

Ko da yake kamfanin bai bayyana takamaiman wuraren da gyaran zai shafa ba.

Sai dai gyaran yana da muhimmanci sosai wajen kawo wuta zuwa wasu sassan Legas da maƙwabtanta.

Wannan ya sa jama’a suka fara nuna damuwarsu game da tabbacin samun wuta a lokacin aikin.

Kamfanin ya nemi afuwar jama’a game da matsalolin da za su iya tasowa, inda ya bayyana cewa aikin gyaran ya zama dole domin inganta aikin rarraba wuta a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gyara Lantarki Rarraba Wuta

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin kera manyan motocin dakon kaya na kasar Sin Sinotruk ya kaddamar da motocinsa kirar H2 mai dakon kaya marasa nauyi da ta H3 ta dakon kaya masu matsakaicin nauyi a kasar Kenya, tare da kamfanin CFAO Mobility a matsayin mai rarraba motocin a cikin gida.

Babban manajan kamfanin CFAO Mobility na Sinotruk Sarfraz Premji, ya shaida wa manema labarai a Nairobi, babban birnin kasar Kenya cewa, an kera samfuran motocin ne ne don kawo sauyi ga masana’antar sufuri saboda suna iya daukar kaya masu nauyi, sannan an sa musu manyan tankunan mai, inda hakan zai rage bukatar yawan zuwa shan mai da kuma ba da damar daukar dogon lokaci ana tafiya, kana wannan zai rage yawan kudin da ake kashewa wajen shan mai.

Premji ya ce “bisa tabbatar da ingancin dogaro da su da kuma karkonsu na dogon lokaci, wadannan manyan motocin sun zamo na daban da babu irinsu kuma ababen zabi a cikin nau’o’in manyan motoci masu dakon kaya masu karami da matsakaicin nauyi.”

Ya kuma yi nuni da cewa, ana samun karuwar rungumar manyan motocin kasar Sin a kasuwannin kasar Kenya ne, saboda suna dacewa da titunan mota na Afirka. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Fara Zaman Jin Ra’ayoyin Jama’a Kan Sauya Kundin Tsarin Mulki A Kano
  • Dole gyaran kundin tsarin mulki ya haɗa kan ƙasa da shugabanci na gari — Abba
  • Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta
  • Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50
  • Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya
  • ‘Yan Tawayen Sudan Ta Kungiyar Rapid Support Forces Sun Kashe Mutane 27 A Yammacin Jihar Kordofan Ta Kasar Sudan
  • Anacláudia Rossbach: Ya Kamata Kasashen Afirka Su Koyi Darasi Daga Sin Na Kawar Da Talauci Da Kyautata Kauyuka Zuwa Birane
  • Jirgin Rasha mai dauke da mutum 50 ya yi hatsari a China
  • Ayatullahi Makarem Shirazi Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Hadin kai Da Suka Bayar Lokacin Yakin Kwanaki 12