Aminiya:
2025-09-17@21:51:01 GMT

Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCN

Published: 26th, July 2025 GMT

Wasu yankuna a Jihar Legas, na iya fuskantar rashin wuta na tsawon kwanaki 25, yayin da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN), zai fara gyaran layin lantarkin Omotosho zuwa Ikeja ta Yamma mai ƙarfin 330kV.

A cewar sanarwar da kamfanin ya fitar a ranar Juma’a, 25 ga watan Yuli, aikin zai gudana kowace rana daga ƙarfe 8 na safe zuwa 5 na yamma, kuma za a kammala aikin a ranar Alhamis, 21 ga watan Agustan 2025.

Wani mutum ya buɗe Ofishin Jakadancin Indiya na bogi a ƙasar Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji

Kamfanin, ya bayyana cewa gyaran zai shafi raba wutar lantarki a wasu wurare, kuma hakan na iya janyo ɗaukewar wuta.

Sanarwar ta ce: “Abokan hulɗarmu za su iya fuskantar yawan ɗaukewa da ƙarancin wuta a wasu lokuta saboda aikin gyaran da za a yi.”

Ko da yake kamfanin bai bayyana takamaiman wuraren da gyaran zai shafa ba.

Sai dai gyaran yana da muhimmanci sosai wajen kawo wuta zuwa wasu sassan Legas da maƙwabtanta.

Wannan ya sa jama’a suka fara nuna damuwarsu game da tabbacin samun wuta a lokacin aikin.

Kamfanin ya nemi afuwar jama’a game da matsalolin da za su iya tasowa, inda ya bayyana cewa aikin gyaran ya zama dole domin inganta aikin rarraba wuta a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gyara Lantarki Rarraba Wuta

এছাড়াও পড়ুন:

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

An garzaya da shi zuwa babban Asibitin Gwamnatin Tarayya da ke Birnin Kebbi, inda daga bisani likitoci suka tabbatar da rasuwarsa.

An yi jana’izarsa a babban masallacin Sarkin Gwandu, sannan aka binne shi a makabartar Dukku da ke kan hanyar Makera zuwa Kangiwa.

Jana’izar ta samu halartar jami’an kwas5tan, ‘yan uwa, abokai da sauran mu5sulmi daga sassa daban-daban na jihar.

Har yanzu al’ummar garin Filgila da kewaye na cikin tashin hankali da fargaba, kasancewar hare-haren Lakurawa na jefa su cikin zulumi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin
  • Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki