Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCN
Published: 26th, July 2025 GMT
Wasu yankuna a Jihar Legas, na iya fuskantar rashin wuta na tsawon kwanaki 25, yayin da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN), zai fara gyaran layin lantarkin Omotosho zuwa Ikeja ta Yamma mai ƙarfin 330kV.
A cewar sanarwar da kamfanin ya fitar a ranar Juma’a, 25 ga watan Yuli, aikin zai gudana kowace rana daga ƙarfe 8 na safe zuwa 5 na yamma, kuma za a kammala aikin a ranar Alhamis, 21 ga watan Agustan 2025.
Kamfanin, ya bayyana cewa gyaran zai shafi raba wutar lantarki a wasu wurare, kuma hakan na iya janyo ɗaukewar wuta.
Sanarwar ta ce: “Abokan hulɗarmu za su iya fuskantar yawan ɗaukewa da ƙarancin wuta a wasu lokuta saboda aikin gyaran da za a yi.”
Ko da yake kamfanin bai bayyana takamaiman wuraren da gyaran zai shafa ba.
Sai dai gyaran yana da muhimmanci sosai wajen kawo wuta zuwa wasu sassan Legas da maƙwabtanta.
Wannan ya sa jama’a suka fara nuna damuwarsu game da tabbacin samun wuta a lokacin aikin.
Kamfanin ya nemi afuwar jama’a game da matsalolin da za su iya tasowa, inda ya bayyana cewa aikin gyaran ya zama dole domin inganta aikin rarraba wuta a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gyara Lantarki Rarraba Wuta
এছাড়াও পড়ুন:
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya
Kamfanin kera manyan motocin dakon kaya na kasar Sin Sinotruk ya kaddamar da motocinsa kirar H2 mai dakon kaya marasa nauyi da ta H3 ta dakon kaya masu matsakaicin nauyi a kasar Kenya, tare da kamfanin CFAO Mobility a matsayin mai rarraba motocin a cikin gida.
Babban manajan kamfanin CFAO Mobility na Sinotruk Sarfraz Premji, ya shaida wa manema labarai a Nairobi, babban birnin kasar Kenya cewa, an kera samfuran motocin ne ne don kawo sauyi ga masana’antar sufuri saboda suna iya daukar kaya masu nauyi, sannan an sa musu manyan tankunan mai, inda hakan zai rage bukatar yawan zuwa shan mai da kuma ba da damar daukar dogon lokaci ana tafiya, kana wannan zai rage yawan kudin da ake kashewa wajen shan mai.
Premji ya ce “bisa tabbatar da ingancin dogaro da su da kuma karkonsu na dogon lokaci, wadannan manyan motocin sun zamo na daban da babu irinsu kuma ababen zabi a cikin nau’o’in manyan motoci masu dakon kaya masu karami da matsakaicin nauyi.”
Ya kuma yi nuni da cewa, ana samun karuwar rungumar manyan motocin kasar Sin a kasuwannin kasar Kenya ne, saboda suna dacewa da titunan mota na Afirka. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp