Aminiya:
2025-09-17@23:26:15 GMT

Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno

Published: 24th, July 2025 GMT

Dakarun Sojin Operation Hadin Kai, sun daƙile hare-haren Boko Haram a garuruwan Monguno da Bitta da ke Jihar Borno, tare da wani kashe babban Kwamandan Boko Haram mai suna Ibn Khalid.

Sun kuma kashe ’yan ta’adda da dama, ciki har da wani babban kwamandan ƙungiyar.

NAJERIYA A YAU: Cututtukan da rumar daki ke haifarwa ga jikin mutum Tinubu ya sake miƙa buƙatar karɓo bashin Dala miliyan 347 daga ƙetare

Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar, Kapten Reuben Kovangiya, ya ce sojojin sun yi jarumta wajen hana ’yan ta’addan shiga Monguno.

Ya ce sojojin sun yi amfani da manyan makamai wajen mayar da martani, inda suka kashe ‘yan ta’adda da dama, ciki har da wani babban kwamandan Boko Haram mai suna Ibn Khalid.

Yayin da sojojin ke bin sahun ’yan ta’addan da suka tsere, sun ga jini a hanya, alamar cewa wasu daga cikinsu sun jikkata.

Sojojin sun kuma ƙwato makamai da dama daga hannun ’yan ta’addan, ciki har da harsasai, PKT, ma’ajin bindiga AK-47, bam ɗin roka (RPG) da wasu kayayyaki.

Haka kuma, sun samu na’urar ɗaukar bidiyo da ’yan ta’addan ke amfani da ita.

A wasu hare-haren daban da suka gudana a wannan lokaci, sojojin sun kashe ƙarin mayaƙan Boko Haram 17 a dazukan Sambisa, Madagali da Kaga.

Haka kuma sun ƙwato babura da wasu kayan amfani daga hannunsu.

Shugabannin dakarun sun yaba da jarumtar sojojin, kuma sun buƙace su da su ci gaba da yaƙar ’yan ta’addan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda Boko Haram kwamanda yan ta addan

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.

 

Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.

Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.

NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

A kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa