Iran Ta Jaddada Wajabcin Daukan Matakin Kawo Karshen Dakatar Da Laifukan Kisan Kare Dangi A Gaza
Published: 25th, July 2025 GMT
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta jaddada cewa: Dole ne kasashen duniya su dauki matakin dakatar da kisan kare dangi a Gaza
Mataimakin shugaban kasar Iran na farko Muhammad Reza Aref ya jaddada cewa: Dole ne a kawo karshen kisan gillar da yahudawan sahayoniyya suke yi a yankin Zirin Gaza cikin gaggawa ta hanyar daukar matakai na zahiri da kuma dauri daga kasashen duniya.
Aref ya rubuta a shafinsa na X a jiya Alhamis cewa: “Mutuwar mutanen da ba su ji ba ba su gani ba saboda yunwa sakamakon hana isar da abinci ga al’ummar Gaza da aka zalunta ya kasance tare da yin shiru na kunya daga kungiyoyin kare hakkin bil’adama na kasa da kasa.”
Ya kara da cewa: “Dole ne a kawo karshen wannan kisan kiyashi da ake yi a fili ta hanyar daukar matakai na zahiri da kasashen duniya zasu dauka, sannan kuma a hukunta wadanda suka aikata wannan laifin na cin zarafin bil’adama.”
Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu a Zirin Gaza ta sanar a cikin wata sanarwa cewa: A cikin sa’o’i 24 da suka gabata an kashe mutane 89 a zirin Gaza, yayin da wasu 453 suka jikkata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An yanke wa mutum 3 hukuncin kisa kan kisan kai a Gombe
Babbar Kotun Jiha a Gombe mai lamba ta 3 ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wasu mutum uku bisa laifin haɗa baki da kuma kisan kai.
Alƙalin kotun Mai shari’a Haruna Kereng ne ya jagoranci shari’ar, inda ya ce kotu ta sami Dauda Mohammed Abubakar (wanda aka fi sani da Agenda) da Kabiru Abubakar (Gwarei) da Ibrahim Suleiman da laifi a kan dukkanin tuhume-tuhumen da ake musu dangane da kisan Ibrahim Yahaya a unguwar Herwagana da ke Ƙaramar Hukumar Gombe a ranar 22 ga Afrilu, 2022.
An kai hari a ƙauyuka uku da kashe mutum 7 a Imo An kashe mata da yara a sabon harin FilatoKotun ta ji cewa, mutanen ukun sun kai wa Ibrahim Yahaya hari ɗauke da makamai masu haɗari kamar: takubba da wuƙa, inda suka kashe shi tare da jikkata wasu mutane biyu, wato Ahmed Abubakar da Muhammad Ahmed Lawan a lokacin harin.
Shari’ar ta fara tun ranar 17 ga watan Nuwamba, 2022, kuma an kammala ta a ranar Laraba, 24 ga Yuli, 2025.
Kereng ya bayyana cewa masu gabatar da ƙara sun gabatar da hujjoji masu ƙarfi da suka tabbatar da laifin da waɗanda ake tuhuma suka aikata, kamar yadda doka ta tanada a sashe na 97 da 221 na dokar laifuka, wanda ta tanadar da hukuncin kisa ga wanda aka same shi da laifin haɗa baki da kuma kisan kai.
Yayin da yake yanke hukunci, Mai sharia Kereng ya ce “Kowannen ku za a rataye shi a wuyansa har sai an tabbatar da mutuwarsa ta hanyar gwajin likita.”
Ya kara da cewa kotu ba ta da ikon rage hukuncin, don haka ba ta saurari roƙon sassauci ba.