Aminiya:
2025-09-17@21:53:16 GMT

Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa

Published: 24th, July 2025 GMT

Matukar ba a sami sauyin tsare-tsare ba, akwai yiwuwar Ministan Jinkai da Yaki da Talauci, Farfesa Nentawe Yilwatda ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na kasa a yau Alhamis.

Majiyoyi da dama a daren jiya sun shaida wa Aminiya cewa Nentawe ne ke kan gaba a cikin mutanen da ake so su dare shugabancin jam’iyyar mai mulki.

Sai dai a cewar wasu majiyoyin, tsohon Gwamnan Jihar Nasarawa, Sanata Umaru Tanko Almakura shi ma na daga cikin wadanda ake duba yiwuwar ba kujerar.

Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno NAFDAC ta gano dakin ajiye kayayyaki makare da sinadaran hada bam a Kano

A daidai lokacin da ya rage ’yan sa’o’i gabanin taron Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar, majiyoyi da dama sun shaida mana cewa shugabancin jam’iyyar, wanda ya kunshi Shugaban Kasa da Gwamnoni sun yanke shawarar takaita neman wanda zai hau kujerar tsakan Nentawe da Almakura.

Nentawe dai dan asalin jihar Filato ne da ke shiyyar Arewa da Tsakiya, yankin da aka tsara zai fitar da shugaban jam’iyyar kafin daga bisani a nada tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, wanda ya ajiye mukaminsa a farkon wannan watan.

To sai dai majiyoyin sun ce an saka sunan Almakura ne a matsayin zabi na biyu.

Tun bayan saukar Ganduje dai ’yan shiyyar Arewa ta Tsakiya ke ta hankoron ganin an dawo da kujerar yankinsu, kasancewar dan cikinsu, wato Sanata Abdullahi Adamu ne ke kanta kafin ya sauka bayan nasarar Shugaba Tinubu a zaben 2023.

Bayanai sun nuna sai da aka yi dogon nazari kafin a yanke shawarar dauko dan yankin kuma Kirista, saboda a hakurkurtar da wadanda zabin Musulmai guda biyu, Tinubu da Kashim, ya bakantawa.

Duk wanda ya yi nasarar dai shi ne zai karbi ragamar da shugabanta na riko na yanzu, Ali Bukar Dalori, wanda mataimakin shugaba ne kafin saukar Ganduje.

Wasu dai na cewa da shi aka kyale ya ci gaba, amma wata majiyar ta ce kasancewarsa daga jiha daya da Kashim sannan kuma Tinubu na so a yi ta ta kare a kan batun shugabancin ya sa dole a zabo wani.

Wata majiyar kuma ta ce, “Tinubu na san wani dan-a-mutun shi ya zama shugaban kamar yadda Abdullahi Adamu ya kasance zamanin Buhari”.

Sauran wadanda a baya aka yi ta rade-radin za su hau kujerar sun hada da Sanata Sani Musa (Neja) da Sanata Salihu Mustapha (Kwara) da Sanata Joshua Dariye (Filato) da Sanata George Akume (Binuwai) da kuma Sanata Abu Ibrahim (Katsina).

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nentawe Yilwatda

এছাড়াও পড়ুন:

Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza

Kasashen duniya na ci gaba da yin tir da sabon farmakin soji da Isra’ila ta kaddamar kan Gaza.

Kasashen Biritaniya, Faransa, Italiya, Masar, Jordan, Qatar, Spain, duk sun yi tir da farmakin kan Gaza suna masu cewa zai kara dagula halin kunci da ake ciki.

Kungiyar tarayyar Turai, ta bakin Jami’ar kula da harkokin wajen  ta, Kaja Kalas, ta yi kira da a sanyawa Isra’ila takunkumi domin matsa wa gwamnatin lamba ta kawo karshen hare-haren da take kaiwa Gaza, tana mai gargadin cewa al’amuran jin kai na kara ta’azzara.

“Hare-haren da Isra’ila ta kai a Gaza zasu haifar da mummunan sakamako game da halin da ake ciki da karin hasarar rayuka, da barna & hijira na jama’a,” in ji Kalas a kan X.

A jiya ne Sojojin Isra’ila suka kaddamar da sabon farmakin ta kasa mai manufar mamaye birnin Gaza bayan shafe makwanni ana kai hare-haren bama-bamai ba kakkautawa ba a kan wasu manyan gine-gine domin tilastawa Falasdinawa kauracewa gidajensu.

Farmakin ya zo ne jim kadan bayan da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya gana da firaminista Benjamin Netanyahu a kusa da masallacin Al Aqsa da ke gabashin birnin Kudus da aka mamaye.

Tun da farko dai, wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman kan yankunan Falasdinawa da ke mamaye, Francesca Albanese ta yi Allah wadai da hare-haren da Isra’ila ke kai wa birnin Gaza, tana mai cewa wani bangare ne na shirin Isra’ila na shafe Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza
  • Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)