Aminiya:
2025-11-02@00:51:28 GMT

Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa

Published: 24th, July 2025 GMT

Matukar ba a sami sauyin tsare-tsare ba, akwai yiwuwar Ministan Jinkai da Yaki da Talauci, Farfesa Nentawe Yilwatda ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na kasa a yau Alhamis.

Majiyoyi da dama a daren jiya sun shaida wa Aminiya cewa Nentawe ne ke kan gaba a cikin mutanen da ake so su dare shugabancin jam’iyyar mai mulki.

Sai dai a cewar wasu majiyoyin, tsohon Gwamnan Jihar Nasarawa, Sanata Umaru Tanko Almakura shi ma na daga cikin wadanda ake duba yiwuwar ba kujerar.

Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno NAFDAC ta gano dakin ajiye kayayyaki makare da sinadaran hada bam a Kano

A daidai lokacin da ya rage ’yan sa’o’i gabanin taron Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar, majiyoyi da dama sun shaida mana cewa shugabancin jam’iyyar, wanda ya kunshi Shugaban Kasa da Gwamnoni sun yanke shawarar takaita neman wanda zai hau kujerar tsakan Nentawe da Almakura.

Nentawe dai dan asalin jihar Filato ne da ke shiyyar Arewa da Tsakiya, yankin da aka tsara zai fitar da shugaban jam’iyyar kafin daga bisani a nada tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, wanda ya ajiye mukaminsa a farkon wannan watan.

To sai dai majiyoyin sun ce an saka sunan Almakura ne a matsayin zabi na biyu.

Tun bayan saukar Ganduje dai ’yan shiyyar Arewa ta Tsakiya ke ta hankoron ganin an dawo da kujerar yankinsu, kasancewar dan cikinsu, wato Sanata Abdullahi Adamu ne ke kanta kafin ya sauka bayan nasarar Shugaba Tinubu a zaben 2023.

Bayanai sun nuna sai da aka yi dogon nazari kafin a yanke shawarar dauko dan yankin kuma Kirista, saboda a hakurkurtar da wadanda zabin Musulmai guda biyu, Tinubu da Kashim, ya bakantawa.

Duk wanda ya yi nasarar dai shi ne zai karbi ragamar da shugabanta na riko na yanzu, Ali Bukar Dalori, wanda mataimakin shugaba ne kafin saukar Ganduje.

Wasu dai na cewa da shi aka kyale ya ci gaba, amma wata majiyar ta ce kasancewarsa daga jiha daya da Kashim sannan kuma Tinubu na so a yi ta ta kare a kan batun shugabancin ya sa dole a zabo wani.

Wata majiyar kuma ta ce, “Tinubu na san wani dan-a-mutun shi ya zama shugaban kamar yadda Abdullahi Adamu ya kasance zamanin Buhari”.

Sauran wadanda a baya aka yi ta rade-radin za su hau kujerar sun hada da Sanata Sani Musa (Neja) da Sanata Salihu Mustapha (Kwara) da Sanata Joshua Dariye (Filato) da Sanata George Akume (Binuwai) da kuma Sanata Abu Ibrahim (Katsina).

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nentawe Yilwatda

এছাড়াও পড়ুন:

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Sai dai don neman cimma burinta na “sake mayar da kasar Amurka zakaran gwajin dafi”, kasar Amurka ta sha daukar matakai na dakile ci gaban kasar Sin, ciki har da katse huldar tattalin arziki da ita da ma sanya takunkumai ga kamfanoninta masu ci gaban kimiyya da sauransu, duk da hakan, kasar Sin ta kiyaye bunkasar tattalin arzikinta yadda ya kamata, har ma karuwar tattalin arzikinta ta kai kaso 5.2% a cikin watanni tara na farkon bana, lamarin da ya shaida inganci da juriya na tattalin arzikin kasar. A kwanan nan, kasar Sin ta zartas da shawarwarin da aka gabatar game da tsara shirin raya tattalin arziki da zaman al’umma cikin shekaru biyar masu zuwa, kuma bisa ga shawarwarin, za a tsara shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15 na kasar. Cikin sama da shekaru 70 da suka wuce, kasar Sin ta yi ta kokarin aiwatar da shirye-shiryen ba tare da kasala ba, ba don neman kalubalantar wata ko maye gurbinta ba, amma don mai da hankali a kan raya kanta da kuma bayar da damammaki na samun ci gaba ga sauran kasashen duniya.

 

Ganawar da aka yi a wannan karo ta kasance ta farko a tsakanin shugabannin kasashen biyu tun bayan da shugaba Trump ya sake hawa karagar mulkin kasar Amurka. Kafin wannan kuma, shugabannin biyu sun taba tattaunawa da juna ta wayar tarho har sau uku, don nuna alkiblar bunkasar huldar kasashensu. Tun bayan watan Mayun da ya gabata, bisa daidaiton da shugabannin biyu suka cimma, tawagogin kasashen biyu sun gudanar da shawarwarin tattalin arziki da cinikayya har sau biyar. A sabon zagayen shawarwarin da aka gudanar a baya bayan nan a birnin Kuala Lumpur, sassan biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan batutuwan tattalin arziki da ciniki da ke janyo hankulansu duka, tare da cimma matsaya daya a kan matakan da za a dauka. Lallai ta hanyar yin shawarwari da juna cikin daidaito, sassan biyu sun kai ga karfafa fahimtar juna da amincewa da juna, hakan kuma ya shaida cewa, yin shawarwari da juna ya fi yin gaba da juna, kuma Sin da Amurka suna iya raya kansu tare da tabbatar da ci gabansu na bai daya.

 

Kasancewarsu kasashe biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, alhakin da ke rataya a wuyan Sin da Amurka ne su gano hanyar da ta dace ta cudanya da juna. Kasashen biyu za su iya karfafa ginshikin huldarsu da samar da kyakkyawan yanayi na bunkasa kansu, tare da samar da karin tabbas da kwarin gwiwa ga duniya, muddin sun tabbatar da daidaiton da shugabanninsu suka cimma, kuma suka yi hangen nesa tare da nacewa ga yin shawarwari da juna wajen daidaita sabaninsu, da kuma inganta hadin gwiwarsu da mu’amala da juna a kai a kai.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayinmu Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu October 17, 2025 Ra'ayinmu Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai October 10, 2025 Ra'ayinmu Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan September 7, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai
  • Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
  • Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar
  • Tinubu ya ƙirƙiri sabon harajin da zai iya ƙara N100 a kan kowacce litar man fetur
  • An Kafa Dokar Ta Baci A Birnin Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa