Tsohon shugaban jami’ar Kashere ya rasu a Abuja
Published: 27th, July 2025 GMT
Allah Ya yi wa tsohon shugaban Jami’ar Tarayya ta Kashere da ke Jihar Gombe, Farfesa Alhassan Gani, rasuwa a safiyar Lahadi a wani asibiti da ke Abuja.
Ya rasu yana da shekaru 66 a duniya.
Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP Gwamna Bauchi ya sasanta manoma da makiyaya a DarazoKafin rasuwarsa, Farfesa Gani yana koyarwa a Sashen Kimiyyar Halittu na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi.
Farfesa Gani, ya yi fice wajen sadaukar da kansa wajen ci gaban ilimi, musamman lokacin da yake jagorantar Jami’ar Kashere.
Gwamna Inuwa Yahaya ya aike da saƙon ta’aziyyarsaGwamnan Jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayyana rasuwar Farfesan a matsayin babban rashi ga harkar ilimi da Najeriya baki ɗaya.
A wata sanarwa da mai magana da yawun gidan gwamnati, Ismaila Uba Misilli, ya fitar, ya ce Farfesa Gani ya taka rawar gani wajen bunƙasa Jami’ar Kashere.
“Farfesa Gani malami ne na ƙwarai, jagora kuma abin koyi wanda ya taimaka wa ɗalibai da jami’a. Mutuwarsa babban giɓi ne.”
Gwamnan ya yi addu’ar Allah Ya gafarta masa, Ya sa aljanna ce makomarsa, tare da bai wa iyalansa da abokan aikinsa haƙuri da juriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farfesa Gani rasuwa Farfesa Gani
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
Namadi ya bayyana fatan cewa ayyukan hukumar ta Hisbah za su kawo kyakkyawan tsarin zamantakewa da tarbiyya a jihar.
Ya kuma bukaci jami’an Hisba da su gudanar da ayyukansu cikin tsoron Allah, adalci, da sadaukarwa.
Gwamnan ya kuma yaba wa ‘yan kwamitin kafa hukumar Hisbah bisa jajircewa, kwazon da suka yi, da sadaukarwa wajen gudanar da aikin da aka dora musu.
“Kokarin da suka yi ya taka rawar gani wajen ganin an aiwatar da kudurin,” in ji shi.
Ya kara da cewa, “Tare da sanya hannu kan wannan doka, a yanzu hukumar Hisbah ta samu cikakken ikon gudanar da ayyukanta a fadin Jihar Jigawa bisa aikinta na inganta kyawawan halaye, tabbatar da adalci ga al’umma, da kyautata rayuwar al’umma.
“Kafa Hisbah a matsayin hukuma babu shakka za ta inganta ayyukanta wajen inganta kyawawan dabi’u da adalci a cikin al’umma a jihar.
“Ana sa ran ayyukan hukumar za su yi tasiri mai kyau ga al’umma.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp