Aminiya:
2025-11-03@09:58:30 GMT

Haaland zai yi jinyar mako bakwai — Guardiola

Published: 1st, April 2025 GMT

Kociyan Manchester City, Pep Guardiola, ya ce ɗan wasan gaban ƙungiyar, Erling Haaland, zai yi jinyar mako bakwai a sakamakon raunin da ya samu a idon sahunsa a wasan kofin FA da ƙungiyar ta fafata da Bournemouth a ranar Lahadi.

Ɗan wasan na ƙasar Norway bai ƙarasa wasan ba, inda aka cire shi a minti 61 da fara wasan bayan ya farke ƙwallo ɗaya, kafin daga bisani City ta doke Bournemouth da ci biyu da ɗaya domin zuwa wasan kusa da na ƙarshe.

HOTUNA: Sarki Sanusi ya kai wa Abba ziyarar barka da Sallah Gangamin da zan yi a mazaɓata babu fashi — Natasha

Tun a jiya Litinin ce City ta ce Haaland zai ga ƙwararren likita saboda raunin da ya ji rauni, kuma tana sa ran zai warware ya ci gaba da taka leda a wannan kakar da ake ciki.

Sai dai a yau Talata gabanin wasan da City za ta fafata da Leicester City a Firimiyar Ingila, Guardiola ya sanar da cewa likitocin sun tabbatar da cewa ɗan wasan zai yi jinyar mako biyar zuwa bakwai kafin ya iya dawowa taka leda a Etihad.

A bayan nan dai City na fuskantar cakwakwiyar ’yan wasa da ke fama da jinya, ciki har da Rodri wanda ya lashe kambun gwarzon ɗan wasa ta Balon d’Or a bara.

A yanzu dai City ba ta wani ɗan wasa da zai iya maye gurbin Haaland, amma Guardiola ya ce ƙungiyar za ta ƙarasa kakar wasannin a daddafe a haka kuma za ta jajirce don samun gurbin zuwa Gasar Zakarun Turai mai zuwa.

A halin yanzu City mai maki 48 na mataki na biyar a teburin Firimiyar Ingila yayin da ya rage mata wasanni tara da kuma wasan mataki na biyun ƙarshe a Kofin FA da za ta kece raini da Nottingham Forest a wannan wata na Afrilu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Erling Haaland Pep Guardiola

এছাড়াও পড়ুন:

Maganin Nankarwa (3)

Yawan shafa man kade a wurin ma yana rage ta sosai.

Daga karshe Ina kira ga mata da su daure da zarar sun haihu su fara neman hanyan magance wannan matsalar kuma ku sani cewa wannan hadin gargajiya ne babu Kemikal a cikinsa don haka yana daukar lokaci kafin a ga canji kamar, sati biyu idan ba ki ga canji ba sai ki dauki wani kuma.

Allah shi ne masani. Allah yasa mu dace.

Ga hanyoyi guda 5 da za’a iya magance su a saukake ba tare da amfani da mayuka masu illlata fata ba

Hanya ta 1: Dankalin Hausa

Dankali yana dauke da sinadarin sitaci da yake lausasa fata da kuma sinadarin da yake hana fata lalacewa wato antiodidant. Haka kuma dankali yana dauke da sinadarin bitamin C, potassium, thiamin, riboflabin, iron, zinc da sauran su.

Yanda ake amfani da shi:

A yanka Dankali sannan a shafa a hankali a kan Nankarwar. Sai a bar shi na tsawon mintuna 15 zuwa 20, sannan a wanke da ruwan dumi. A maimaita haka a kullum

Hanya ta 2: Alo bera

Ruwan da ke cikin Alo bera yana dauke da sinadarin Collagen wanda aka san shi da gyara fatar da ta lalace da kuma kara laushin ta, kyanta da kuma yarintar ta.

Yanda ake amfani da shi:

A karya itacen Alo bera guda sai a shafa ruwan a kan Nankarwa. A bar shi tsawon awa 2 zuwa uku sai a wanke da ruwa. A maimata hakan a kullum har sai an samu sakamako mai kyau.

Hanya ta 3: Man kadanya da koko Bota

Hadin man kadanya da koko Bota yana dauke da sinadarin bitamin E da kuma sinadaran da ke hana fata lalacewa

Yadda ake amfani da shi

Za’a samu Koko Bota karamin cokali 2, da man kadanya shima karamin cokali 2, sai sinadarin Bitamin E karamin cokali 1. Za’a narka man kadanya da kuma man koko Bota sai a kara bitamin E din a ciki a gauraya. Za’a dura gaba daya a cikin mazubi a ajiye ana shafawa a kan Nankarwar kullum.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa November 2, 2025 Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025 Labarai Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Maganin Nankarwa (3)
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa