Aminiya:
2025-07-25@23:29:42 GMT

Hulk Hogan ya mutu yana da shekara 71

Published: 24th, July 2025 GMT

Shahararren ɗan kokawa ɗan ƙasar Amurka mai ritaya Terry Gene Bollea wanda aka fi sani da Hulk Hogan ya rasu yana da shekara 71 a duniya.

A cewar TMZ da sauran rahotanni, likitoci sun mayar da martani a gidansa na Clearwater, da ke Florida da sanyin safiyar Alhamis kan Hulk Hogan ya kamu da bugun zuciya da ya yi ajalinsa.

An rantsar da Nentawe sabon shugaban APC na ƙasa Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja

Daga nan an ɗauki Hogan da wuri aka saka shi cikin motar ɗaukar marasa lafiya.

Duk da damuwa na kwanan da aka bayyana game da lafiyarsa – ciki har da larurar wuyansa a farkon wannan shekara, matarsa ​​Sky ta riga ta ce zuciyarsa ta kasance tana bugu da ƙarfi.

Hogan ya kasance mutum mai kawo sauyi a cikin ƙwararrun ‘yan kokawa, wanda aka yaba wa wajen  ɗaga darajar wasan da nishaɗantarwa.

Ya fara wasa a bainar jama’a a cikin shekarar 1977 kuma ya fara zama babban tauraro a cikin 1980s tare da Kamfanin nishaɗantarwar kokawa na WWE (yanzu ya zama WWE), yana ba da labarin abubuwan da suka faru kuma ya zama zakaran WWF sau shida.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

‎Sarkin Katsinan Gusau ya rasu

‎Allah ya yi wa Sarkin Katsinan Gusau da ke jihar Zamfara, Dr Ibrahim Bello rasuwa.

Ya rasu da safiyar Juma’a a Abuja yana da shekaru 71, bayan ya sha fama da jinya.

Yadda aka mayar da yaran da aka sace a Kano masu wanke-wanke a Kudu An kama budurwa mai shekara 19 da ake zargi da kashe yara 2 a Bauchi

Marigayin, wanda shi ne Sarkin Gusau na 16, ya ɗare kan karaga ne a shekara ta 2015, bayan rasuwar mahaifinsa.

Gogaggen ma’aikacin gwamnati, Dr Ibrahim ya taɓa zama Babban Sakatare a tsohuwar jihar Sakkwato da ma jihar Zamfara.

‎Ya yi mulkin ne na tsawon shekara 10 da ’yan watanni kafin rasuwar tasa.

Da yake tabbatar da rasuwar, Kakakin Gwamna Dauda Lawal na jihar ta Zamfara, Sulaiman Idris, a jajanta wa mutanen jihar a kan rasuwar.

A cikin wata sanarwa da safiyar Juma’a, Gwamnan ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi a wajensa, inda ya ce Sarkin ya tsaya tsayin daka wajen ci gaban jihar.

Daga nan sai ya yi addu’a Allah ya jikan mamacin ya kuma ba iyalansa da ma al’ummar jihar haƙurin jure rashin sa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
  • Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya
  • ‎Sarkin Katsinan Gusau ya rasu
  • Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau
  • Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (4)
  • Ina Karanta Rantsuwar Da Na Yi A Kullum Don Tuna Nauyin Da Ke Kaina-Gwamna Namadi
  • Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa
  • Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa
  • Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu