Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Dashen Itatuwa Na Bana
Published: 27th, July 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta kaddamar da dashen itatuwa na shekarar 2025 tare da sabunta kudirin farfado da fiye da hekta 5,000 da ta lalace a fadin jihar.
Gwamna Umar Namadi ne ya bayyana haka a wajen bikin kaddamar da shirin da aka gudanar a shatale-tale na Pentagon da ke Dutse babban birnin jihar.
Ya bayyana aikin dashen itatuwan a matsayin ɗaya daga cikin alkawuran da gwamnatinsa ta ɗauka domin ci gaban al’umma, inda ya ce gwamnatin sa za ta ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen raya muhalli da kare shi.
Ya ce: “Wannan yana da alaƙa da manufofinmu da suka shafi ƙaddamar da tsare-tsare da suka dace da kare muhalli, da ƙarfafa juriya da dorewar muhalli, da kuma inganta rayuwa mai tsafta da dorewa ga al’umma.”
Yayin da yake bayyana muhimmancin shirin, Malam Umar Namadi ya jaddada cewa kalubalen muhalli kamar ambaliya, sahara, sare itatuwa da kuma rashin daidaiton kula da shara na cigaba da barazana ga rayuwar mutane a jihar.
“Wannan barazana na shafar rayuwarmu ta yau da kullum, abincinmu, lafiyarmu, da kuma zaman lafiyar al’ummomi da dama a fadin jihar. Ya zama wajibi mu hada kai domin yaki da duk wani nau’in lalacewar muhalli.” In ji Gwamnan.
Gwamnan wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim ya wakilta, ya bayyana cewa ana amfani da shirin ACReSAL wajen farfado da ƙasa ta hanyar dasa itatuwa, da kiyayewa da kuma tsarin noma da gandun daji.
“Yanzu haka, gwamnatin jihar Jigawa ta hanyar shirin ACReSAL na kokarin farfado da hekta 5,000 a wurare 27 a fadin jihar, ta hanyar samar da katanga ta itatuwa, wuraren kiwo da tsarin gandun daji. Mun riga mun fara sauya yanayin da ake ciki ta hanyar wadannan matakan da za a iya auna su.”
Ya kuma bayyana cewa an duba dokoki guda biyar da suka shafi muhalli kuma an miƙa su zuwa majalisar dokoki domin gyara.
A cewarsa, dokokin da aka duba sun hada da Dokar Gandun Daji, Dokar Hana Kona Daji, Dokar Kiwon Dabbobi da Dokokin Tsafta.
Gwamna Namadi ya kara da cewa domin rage hadarin ambaliya da sarrafa ruwa, gwamnatin jihar ta sayi injina biyu masu iya aiki a ruwa da ƙasa domin kwance hanyoyin koguna da ciyawar Typha ta toshe.
“Baya ga wannan, gwamnati na aikin gina magudanan ruwa a wurare 32 daban-daban domin farfado da yankunan da ambaliya ta shafa. An kuma gina kilomita 130 na katanga a bakin rafuka domin rage ambaliya, kare gonaki da ƙarfafa ƙarfin gwiwar al’ummomin da ke cikin haɗari.”
Gwamnan ya yi gargaɗi mai ƙarfi ga masu sare itatuwa da masu yin gawayi da su daina, ko kuma su fuskanci fushin doka.
“Ina amfani da wannan dama in gargadi duk masu sare itatuwa ba bisa ka’ida ba, da masu yin gawayi da su daina. Kamar yadda muka ambata, mun duba dokokinmu na muhalli kuma mun tanadi hukunci mai tsauri ga duk wanda ya karya wadannan dokoki.”
Rediyon Najeriya ya bayyana cewa, Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim ne ya jagoranci dashen itatuwan da kuma raba irin shukar ga ƙananan hukumomi.
Wannan wani bangare ne na tsare-tsaren kare muhalli na jihar, wanda ya haɗa da samar da irin itatuwa mmiliyan biyu da rabi a duk shekara, wayar da kai, da kuma haɗin gwiwa da hukumomin ƙasa da na ƙetare.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Itatuwa Jigawa Gwamnatin Jihar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
Gwamnatin mamayar Isra’ila ta yanke hukuncin kisa kan masu fama da cutar kansa da kuma waɗanda suke fama da matsalar koda na mutuwa a Gaza domin hana fitar da su wata kasa don neman magani
Cibiyar Kare Hakkin Dan Adam ta Gaza ta bayyana matukar damuwarta game da tabarbarewar lafiyar marasa lafiya da ke fama da cutar kansa da kuma cutar koda a Zirin Gaza. Wadannan cututtuka sun kara ta’azzara ne sakamakon hare-haren sojojin mamayar Isra’ila kan Gaza da kuma ci gaba da killace yankin bayan tsagaita bude wuta, gami da hana shigar dq magunguna da kayayyakin ayyukan likitanci masu muhimmanci cikin yankin. Cibiyar ta kuma yi nuni da tsauraran matakan fitar da marasa lafiya zuwa ƙasashen waje don neman magani.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, Cibiyar ta tabbatar da cewa, wannan yanayin ba shi da wata shakka cewa Isra’ila na aiwatar da manufar kisan gilla a kan dubban marasa lafiya ta hanyar hana su ‘yancinsu na rayuwa da magani da gangan, da kuma canza wahalarsu zuwa wani nau’in hukunci na gama gari.
Cibiyar ta ambaci majiyoyin lafiya da ke tabbatar da cewa, akwai marasa lafiya 12,500 da ke fama da cutar kansa a Zirin Gaza, ciki har da ƙananan yara. Ta lura cewa mata sun kai kusan kashi 52% na dukkan masu cutar kansa a Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci