Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-27@05:56:45 GMT

Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Dashen Itatuwa Na Bana

Published: 27th, July 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Dashen Itatuwa Na Bana

Gwamnatin Jihar Jigawa ta kaddamar da dashen itatuwa na shekarar 2025 tare da sabunta kudirin farfado da fiye da hekta 5,000 da ta lalace a fadin jihar.

Gwamna Umar Namadi ne ya bayyana haka a wajen bikin kaddamar da shirin da aka gudanar a shatale-tale na Pentagon da ke Dutse babban birnin jihar.

 

Ya bayyana aikin dashen itatuwan a matsayin ɗaya daga cikin alkawuran da gwamnatinsa ta ɗauka domin ci gaban al’umma, inda ya ce gwamnatin sa za ta ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen raya muhalli da kare shi.

Ya ce: “Wannan yana da alaƙa da manufofinmu da suka shafi ƙaddamar da tsare-tsare da suka dace da kare muhalli, da ƙarfafa juriya da dorewar muhalli, da kuma inganta rayuwa mai tsafta da dorewa ga al’umma.”

Yayin da yake bayyana muhimmancin shirin, Malam Umar Namadi ya jaddada cewa kalubalen muhalli kamar ambaliya, sahara, sare itatuwa da kuma rashin daidaiton kula da shara na cigaba da barazana ga rayuwar mutane a jihar.

“Wannan barazana na shafar rayuwarmu ta yau da kullum, abincinmu, lafiyarmu, da kuma zaman lafiyar al’ummomi da dama a fadin jihar. Ya zama wajibi mu hada kai domin yaki da duk wani nau’in lalacewar muhalli.” In ji Gwamnan.

Gwamnan wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim ya wakilta, ya bayyana cewa ana amfani da shirin ACReSAL wajen farfado da ƙasa ta hanyar dasa itatuwa, da kiyayewa da kuma tsarin noma da gandun daji.

“Yanzu haka, gwamnatin jihar Jigawa ta hanyar shirin ACReSAL na kokarin farfado da hekta 5,000 a wurare 27 a fadin jihar, ta hanyar samar da katanga ta itatuwa, wuraren kiwo da tsarin gandun daji. Mun riga mun fara sauya yanayin da ake ciki ta hanyar wadannan matakan da za a iya auna su.”

Ya kuma bayyana cewa an duba dokoki guda biyar da suka shafi muhalli kuma an miƙa su zuwa majalisar dokoki domin  gyara.

A cewarsa, dokokin da aka duba sun hada da Dokar Gandun Daji, Dokar Hana Kona Daji, Dokar Kiwon Dabbobi da Dokokin Tsafta.

Gwamna Namadi ya kara da cewa domin rage hadarin ambaliya da sarrafa ruwa, gwamnatin jihar ta sayi injina biyu masu iya aiki a ruwa da ƙasa domin kwance hanyoyin koguna da ciyawar Typha ta toshe.

“Baya ga wannan, gwamnati na aikin gina magudanan ruwa a wurare 32 daban-daban domin farfado da yankunan da ambaliya ta shafa. An kuma gina kilomita 130 na katanga a bakin rafuka domin rage ambaliya, kare gonaki da ƙarfafa ƙarfin gwiwar al’ummomin da ke cikin haɗari.”

Gwamnan ya yi gargaɗi mai ƙarfi ga masu sare itatuwa da masu yin gawayi da su daina, ko kuma su fuskanci fushin doka.

“Ina amfani da wannan dama in gargadi duk masu sare itatuwa ba bisa ka’ida ba, da masu yin gawayi da su daina. Kamar yadda muka ambata, mun duba dokokinmu na muhalli kuma mun tanadi hukunci mai tsauri ga duk wanda ya karya wadannan dokoki.”

Rediyon Najeriya ya bayyana cewa, Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Bala Ibrahim ne ya jagoranci dashen itatuwan da kuma raba irin shukar ga ƙananan hukumomi.

Wannan wani bangare ne na tsare-tsaren kare muhalli na jihar, wanda ya haɗa da samar da irin itatuwa mmiliyan biyu da rabi a duk shekara, wayar da kai, da kuma haɗin gwiwa da hukumomin ƙasa da na ƙetare.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Itatuwa Jigawa Gwamnatin Jihar

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Wannan yana cikin wani tsari na noma da aka kirkiro musamman don masu bukata ta musamman domin su dogara da kansu maimakon rokon hatsi ko neman taimako.

Wannan yana cikin wani tsari na noma da aka kirkiro musamman don masu bukata ta musamman domin su dogara da kansu maimakon rokon hatsi ko neman taimako.

Wakilinmu ya ziyarcj wata kebabbiyar gona dake cikin garin Kaduna, inda gungun wasu manoma da ke fama da lalurori daban-daban irin su makanta da gurguntaka da kurma, suka rungumi sabbin dabarun noma na zamani domin tallafawa rayuwarsu, musamman a wannan damina da aka shiga.

Gonakin da wadanda makafi da guragu ne suke nomawa a duk shekara Sun bayyana cewa suna gudanar da nomansu ne ba tare da wata gudummawa daga gwamnati ba kama da samar musu da takin zamani da sauran kayan noma kamar yadda ake tallafawa Masu lafiya.

A zantawarsa da wakilinmu a cikin gonarsa, Mista William Makiya, wanda ke fama da matsalar gani (makaho), yana noma da huda domin ciyar da iyalinsa. Ya bayyana cewa:

“Ba na gani da idona. Dalilin da yasa nake yin noma shine domin ciyar da iyalina. Ba na yin bara kuma bana san yin bara kwata-kwata rayuwata. Ba na kaunar bara.”

William ya kara da cewa yana jin dadin aikin noma, kuma yana taimakawa makwabtansa masu lafiya da kayan abinci daga gonarsa. Wannan yana karfafa zumunci da hadin kai tsakaninsa da sauran al’umma da suke zaune tare a cikin muhalli daya.

Ya ce:“Da galma nake yin wannan noma. Ina amfani da fatanya da sauran kayan huda wajen noma da kuma cire ciyawa a gonaki.”

Ya ci gaba da cewa gonarsa tana da layukan shuka wanda yake amfani da su wajen shuka wake, dankalin hausa, gyada, da kayan lambu irin su tumatur da kubewa.

A kowace shekara, jajirtattun manoma masu bukata ta musamman ne ke amfani da wadannan filayen noma domin ciyar da kansu, kamar yadda wani matashi mai lalurar kafa Mai Suna Joshua Matthew, ya bayyana cewa Shi ma yana noma da huda a gonarsa.

“Abin da ya kamata a sani shi ne, ni ina noma da huda sosai domin ciyar da iyalina. Ina noma masara da shinkafa da sauran kayayyakin abinci domin rage tsadar rayuwa.”

Joshua ya ce duk da cewa ba shi da kafa, yana zaune yana jan jikinsa domin yin noma da cire ciyawa da sauran ayyukan noma. Ya tabbatar da cewa ya dade yana wannan aiki, kuma babu wahala kamar yadda mutane ke tunani.

Ya jaddada bukatar gwamnati ta tallafa musu domin su zama masu dogaro da kansu.

Duk da karancin ruwan sama a bana, wadannan manoma ba su karaya ba. Sun ci gaba da aiki tukuru a gonakinsu, suna amfani da dabarun noma na zamani domin tabbatar da samun abinci mai yawa da inganci.

Babu shakka, wadannan manoma suna gudanar da aikin noma ta hanyar wani tsarin hada kowa da kowa musamman masu nakasa cikin harkar noma domin yakar yunwa da talauci a Nijeriya. Wannan tsarin na “inclusibe smart farming” ya fara haifar da nasarori, a cewar Kwamared Rilwani Abdullahi, shugaban kungiyar masu bukata ta musamman a Nijeriya.

Ya ce:“Wannan wani yunkuri ne na zama masu dogaro da kai. Saboda haka, muna kira ga hukumomi da su tashi tsaye wajen tallafawa wadannan manoma, da kuma tabbatar da cewa ana sanya su a cikin jerin manoman da ake tallafawa a duk lokacin da ake rabon takin zamani.”

Yanzu haka dai, wadannan gwarazan manoma sun dukufa sosai cikin harkar noma domin ciyar da kansu maimakon barace-barace. Sai dai, sun koka kan yadda ake rarraba takin zamani ba tare da an tuna da su ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
  • Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50
  • Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
  • ALGON Ta Jihar Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da NUJ Don Inganta Kwarewar Aiki
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 3.5 Wajen Gina Shaguna A Farm Centre
  • Jihar Jigawa Na Kara Bullo Da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Bukata Ta Musamman
  • ‘Yan Nijeriya Miliyan 40 Ke Fuskantar Barazanar Kwararowar Hamada – Ministan Muhalli
  • Gwamnatin Yobe ta bada tallafi ga iyalan ’yan banga da suka rasu
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Da Karamar Hukumar Dutse Za Su Shirya Taron Bita Ga Kansiloli