An kama wani matashi da ake zargi da tono gawar kakarsa ta ɓangaren uwa tare da sare kanta da nufin yin tsafin kuɗi a Jihar Naje.

Rundunar ’yan sandan Jihar Neja ta kama mutumin mai shekaru 31 ne bayan dubansa ta cika a yankin.

Kakakin rundunar, Wasiu Abiodun, ya cewa wanda ake zargin tare da abokansa da suka taimaka masa ya tabbatar musu cewa zai yi tsafin kudi ne da ƙwarangwal din tsohuwar.

A cewar kakakin rundunar wanda ake zargin ya furta cewa yana neman tsafin ne don biyan bashin da ya kai sama da Naira miliyan biyu.

Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji Sojoji sun ceto yaro da aka sayar shekaru 3 a Filato

A ranar 19 ga Yuli, 2025 ne jami’an ’yan sanda suka kama wannan gungun mutane da kai a otel ɗin Bida.

Babban wanda ake zargin ya tabbatar cewa kan kakarsa ce mai shekaru sama da 90 a lokacin da ta rasu kimanin shekaru biyu da suka gabata.

Ya ce da farko ya samo kan ne bisa umarnin wani boka, don neman kuɗi cikin hanzari. Amma, bayan jin sharuddan tsafin, ya kasa bi, sai ya ɓoye kan na tsawon shekaru biyu.

Daga baya, abokinsa da wani kuma sun yi masa tayin sayenkan a kan Naira 100,000, kuma suka biya Naira 40,000 a matsayin kuɗin kafin alƙalami.

Daga nan suka kai wani wanda ake zargi da ninka kuɗi, da ya nemi Naira 500,000 don yin tsafin kuma sun biya shi da kaɗan-kaɗan.

Bayan an gama aikin, ya umarce su kada su buɗe ganga har sai ya gaya musu.

Makonni sun shude babu labari ko kuɗi sai suka yi masa takakkiya zuwa gidansa, amma ya shawo kansu cewa su haɗu a wani otel a Bida inda za su karɓi kuɗinsu.

A otel din ne kuma ’yan sanda suka kama su gaba ɗayansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Gawa ƙasarsa Tsohuwa zargi

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu

Hukumar Tsaron Farin Kaya a Nijeriya DSS, ta gurfanar da fitaccen ɗan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore a kotu.

A ƙunshin ƙarar da DSS ta gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta haɗa da shafukan sada zumunta na X da kuma Facebook, inda take zarginsu da ba da ƙofar aibata Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku

Darekan shigar da ƙara na Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya, M.B Abubakar da wasu lauyoyi huɗu —M.E. Ernest da U.B. Bulla da C.S. Eze da kuma E.G. Orubor, ne suka shigar da ƙarar a madadin Gwamnatin Tarayya da kuma hukumar ta DSS.

DSS wadda ta kafa hujja da sashe na 24 da ke cikin kundin dokokin yanar gizo, ta ce Sowore ya yi amfani da shafukansa na dandalan sada zumunta na X da Facebook wajen wallafa wani saƙo da ke cin mutuncin Shugaba Tinubu.

Tun dai a farkon watan nan ne DSS ta buƙaci goge wani saƙo da ɗan gwagwarmayar ya wallafa wanda ta riƙa a matsayin bayanan ƙarya, cin zarafi ta yanar gizo da kalaman haddasa ƙiyayya, waɗanda kuma ta ce na iya haddasa rikici su kuma ɓata sunan Najeriya a ƙasashen waje.

Sai dai har zuwa ranar Litinin, 15 ga watan Satumba, babu wani mataki da aka ɗauka na goge saƙon da DSS ɗin ta buƙata.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar