Matashi ya tono gawar kakarsa don yin tsafin kuɗi ya sare kan gawar kakarsa don yin tsafi
Published: 26th, July 2025 GMT
An kama wani matashi da ake zargi da tono gawar kakarsa ta ɓangaren uwa tare da sare kanta da nufin yin tsafin kuɗi a Jihar Naje.
Rundunar ’yan sandan Jihar Neja ta kama mutumin mai shekaru 31 ne bayan dubansa ta cika a yankin.
Kakakin rundunar, Wasiu Abiodun, ya cewa wanda ake zargin tare da abokansa da suka taimaka masa ya tabbatar musu cewa zai yi tsafin kudi ne da ƙwarangwal din tsohuwar.
A cewar kakakin rundunar wanda ake zargin ya furta cewa yana neman tsafin ne don biyan bashin da ya kai sama da Naira miliyan biyu.
Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji Sojoji sun ceto yaro da aka sayar shekaru 3 a FilatoA ranar 19 ga Yuli, 2025 ne jami’an ’yan sanda suka kama wannan gungun mutane da kai a otel ɗin Bida.
Babban wanda ake zargin ya tabbatar cewa kan kakarsa ce mai shekaru sama da 90 a lokacin da ta rasu kimanin shekaru biyu da suka gabata.
Ya ce da farko ya samo kan ne bisa umarnin wani boka, don neman kuɗi cikin hanzari. Amma, bayan jin sharuddan tsafin, ya kasa bi, sai ya ɓoye kan na tsawon shekaru biyu.
Daga baya, abokinsa da wani kuma sun yi masa tayin sayenkan a kan Naira 100,000, kuma suka biya Naira 40,000 a matsayin kuɗin kafin alƙalami.
Daga nan suka kai wani wanda ake zargi da ninka kuɗi, da ya nemi Naira 500,000 don yin tsafin kuma sun biya shi da kaɗan-kaɗan.
Bayan an gama aikin, ya umarce su kada su buɗe ganga har sai ya gaya musu.
Makonni sun shude babu labari ko kuɗi sai suka yi masa takakkiya zuwa gidansa, amma ya shawo kansu cewa su haɗu a wani otel a Bida inda za su karɓi kuɗinsu.
A otel din ne kuma ’yan sanda suka kama su gaba ɗayansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Gawa ƙasarsa Tsohuwa zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
Don haka nema tayi kira da jama’a kada suyi amfani da shi labarin daya zaman a kanzon kurege da ake ta yadawa,idan wani bayani suke bukata su tuntubi kafa da suka san ba zata yi zuki ta malle ba,ko kuma jami’an ma’aikatar ilimi ta kafar sadarwarsu ko kuma na, WAEC, da NECO.
“An ja hankalin ma’aikatar ilimi ta tarayya akan wani labara ko rahoton da ya karade kafafen sadarwa na zamani,inda aka yi maganar cewar ban soke jarabawar WAEC ta shekarar 2025 da aka yi saboda an samu laifin aikata magudi lokacin da ake yin ta.
“Ma’aikatar tace don haka tana sanar da jama’a cewa ta yi nesa da kanta,dangane da ita sanarwar ko labarin saboda kuwa ai na kanzon kurege ne inda ta kara jaddada: Jarabawar, WAEC ta shekarar 2025,an kammala ta cikin nasara ba tare da wata matsalar data gagara shawo kai ba,in banda wadansu ‘yan kananan laifukan da suka auku,wadanda kuma ita hukumar tayi maganinsu.
“Ita kuma jarabawar NECO ana yinta ba tare da wata matsala ba, ya zuwa kuma hali ko lokacin da ake ciki babu wata matsalar da aka fuskanta. Ma’aikatar ilimi ta tarayya bata samu wani sako ba a hukumance daga WAEC ko kuma NECO,ko kuma duk wata hukuma mai shirya jarabawa da ke nuna an samu aikata magudin jarabawa.”
Ma’aikatar har yanzu babu wani abinda daya tada mata hankali wanda ya wuce aikata lamurran da suka shafi jarabawa cikin gaskiya da rikon amana,da kuma kwanciyar hankali, tana aiki kafada da kafada da su hukumomin jarrabawar,domin a samu inganta yadda ake lura da sa idon dangane da yadda ake gudanar da jarabawar.
Daga karshe ma’aikatar ta kara jaddada ta sha alwashin yadda ake gudanar da jarabawar yayi daidai kamar yadda dokokin hukumar suka bayyana, na samun gaskiya kan duk wata jarabawar da ake yi a Nijeriya,don haka su hukumomin jarrabawar jarabawar abokan huldar ta ne da kuma aiki tare.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp