Yadda za a hada:
Da farko za ki wanke Acca sai ki fid da kasar sai ki ajiye waje guda,
Sannan ki sanya mai a tukunya idan ya yi zafi sai ki sa albasa wadda dama kin gyara ta kin yanka ta sai ki zuba ki soya ta sama-sama ta dan yi ja, sannan ki kawo kayan miyanki wanda dama kin gyara su kin jajjaga su ki zuba ki soya, sannan ki zuba magi, gishiri, kori, tayim sai ki zuba ruwa daidai yadda kika san zai dafa miki ya dahu sannan ki zuba nama sai ki rufe ki bar shi naman ya dahu.
Sannan ki zuba Acca sai ki gauraya ta ki bar ta ki rufe ta na dan mintoci haka ta ci gaba da dahuwa za ki ga tana tukewa.
Da kin kusa saukewa sai ki zuba ganye, za ki yi amfani da duk ganye da kike so, wanda dama kin yanka shi kin wanke, sannan ki juya shi ki rage wuta sosai ki dan bar shi ya dan dahu sai ki sauke. A ci dadi lafiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
Ruwan sama kamar da bakin kwarya hade da iska sun yi ajalin mutum biyar sannan wasu 92 suka samu munanan raunuka a kananan hukumomi bakwai na jihar Yobe.
Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (SEMA) Dr Goje ne ya tabbatar da hakan a ranar Laraba a Damaturu.
Ya ce iftila’in ya shafi al’ummomi 48 ne a fadin kananan hukumomin da lamarin ya faru.
Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka saceDr Goje yan kuma ce bala’in ya shafi gidaje 1,264, tare da raba mutum 5,022 da muhallansu.
Shugaban ya kuma ce hukumarsa tare da hadin gwiwar kungiyar bayar da tallafi ta kasa da kasa ACF tare da tallafi daga ofishin kula da harkokin wajen Jamus (GFFO), sun raba kayan agajin ceton rai ga magidanta 566 a kananan hukumomin Fika da Potiskum da lamarin ya shafa.
Kazalika, kididdigar haɗin gwiwa ta hukumar ta SEMA da ACF suka fitar ta ba da fifiko ga iyalan da wadanda wannan iftila’i ya fi shafa kai tsaye musamman waɗanda suka rasa gidajensu, da kayan masarufi, ko damar samun wani taimakon na tsafta.
Mohammed Liman Kingimi, na kungiyar ACF, ya tabbatar da kudurin kungiyar na kara ba da taimako bisa ga yadda bukatun hakan suka taso.
Ya ce kungiyar na kuma shirye-shiryen kaddamar da tallafin abinci ga magidanta 566 don rage musu radadi.
Dokta Goje ya buqaci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da shi yadda ya kamata sannan ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na kare al’umma masu rauni ta hanyar xaukar matakan gaggawa.
Ya kuma jaddada qudirin hukumar cewa kullum a shirye take wajen gudanar da ayyukanta kamar yadda ya dace.