Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kiran Cewa; Ina Masu Fafatukar Kare Hakkin Dan Adam Suke A Bala’in Gaza?
Published: 27th, July 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya yi kiran cewa: Ina masu fafutukar kare hakkin bil’adama suke a bala’in Gaza?
Shugaban kasar Iran Dr. Masoud Pezeshkian ya jaddada muhimmancin sauya salon tafiyar da gwamnati da kuma karfafa alaka da kasashen da ke makwabtaka da ita, yana mai cewa masu takama da kare hakkin bil’adama suna nuna fuska biyu a aikinsu, inda suka yi shiru kan munanan laifukan da ake yi wa al’ummar Gaza.
A safiyar yau ne shugaba Pezeshkian ya isa ma’aikatar harkokin wajen kasar, inda ya gana da mataimakan ministoci da daraktocin ma’aikatar.
A lokacin da yake jawabi a taron, shugaban ya ce, “Tun da yake dan majalisar shawarar Musulunci bai canza ba, har yanzu shi mutum daya ne, dole ne al’umma su kasance masu jajircewa da kwarewa tare da ci gaba da yin aiki tukuru, sun mika ragamar mulki ga ministoci da gwamnonin larduna, wasu kura-kurai dole ne a gyara su, me yasa gwamna ba zai iya yin abin da shi yake yi ba?”
Pezeshkian ya kara da cewa, “Idan aka bi tsarin manufofin – wato manyan tsare-tsare, kuma aka ba da iko ga wadanda ke cikin wannan fanni, aikin zai ci gaba. Idan kuskure ya faru, dole ne a gyara shi. Daga nan ne yanayin kasar zai inganta.” Dole ne kuma gwamnoni su mika mulki ga shugabannin kananan hukumomi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul
Jami’an diblomasiyya na kasashen Iran da kuma na tarayyar Turai 3 wato Faransa da Jamus da kuma burtaniya sun fara tattaunawa gaba da gaba bayan yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka kai mata.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta kara da cewa wannan tattaunawar yana da matukar muhimmanci don zasu tattauna kan shirin makamashin nukliyar kasar Iran da kuma dauke mata takunkuman tattalin arzikin da su dora mata saboda shirinta na makamshin nukliya. Har’ila yau ana ganin tattaunawar ta Istambul shi zai fayyace makomar dangantaka tsakanin Iran da tarayyar Turai gaba daya nan gaba.
Labarin ya kara da cewa tarunn yana gudana ne a cikin ofishin jakadancin kasar Iran dake birnin Istambul kuma Majid Takht-ravanci da kuma Kazem Ghariba abadi , mataimakin ministan harkokin wajen kasar ta Iran ne zasu jagoranci tawagar Iran a tattaunawar.
Kuma tattaunawar zasu maida hankali ne kan al-amura guda biyu. Shirin nukliyar kasar Iran da kuma dauke mata takunkuman tattalin arziki wadanda turawan suka dora mata.
Kafin taron dai ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa, matsayin Iran bai sawya ba, dole ne tashe makamashin Nukliya a cikin gida ya zama cikin shirin makamashin nukliya na kasar Iran. Ya kuma ce duk wani kokari na amfani da SnapBack zai fuskanci maida martani mai tsanani ga wadannan kasashe.