Mataimakin shugaban kasar Rasha Nikolai Patrushev ya bayyana cewa; duk wani hari da za a kai wa yankin Kalligrad to zai fuskanci mayar da martani mai tsananin gaske.

Mataimakin shugaban kasar ta Rasha ya kuma ce; A bisa akidar tsaro ta Rasha duk wani hari da za a kai mata, to zai sa kasar ta yi amfani da dukkanin makaman da take da su, domin mayar da martani akan abokan gaba, daga ciki har da makaman Nukiliya idan bukatar haka ta taso.

Nikolai Patrushev wanda kamfanin dillancin labarun Sputnik ya yi hira a shi, ya ce;yankin Kallingrad kasar Rasha ne, don haka duk wani hari da za a kai masa zai sa su yi amfani da dukkanin karfin da suke da shi, wajen mayar da martani, har da makaman Nukiliya.

Mataimakin shugaban kasar ta Rasha ta kuma ce; Rasha tana sane da Shirin da kasashen yammacin turai su ke da shi, irin wannan, don haka Rasha tana da makaman da take da bukatuwa da su, domin kare yankin na killingirad.

Nikolai Patrushev ya bayyana shugabanin kasashen yammacin na yanzu da cewa, daidai suke da ‘yan Nazi,don haka za su shiga kwandon sharar tarihi kamar yadda magabatansu ‘yan Nazi na baya su ka shiga.

 A baya kadan ne dai kwamandan sojan Amurka a turai da Afirak janar Chiristopher Donaho ya bayyana cewa; Nato ta shirya yadda za ta raunana layin tsaron da Rasha take da shi a yankin Kallingrad, domin karfafa hanyoyin aiki tare a tsakanin kasashen Nato. 

Shi kuwa mai Magana da yawun fadar shugaban kasar Rasha Dmity Viskov, ya ce; Fadar gwamnatin kasar tana daukar wannan barazanar da hatsari.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: shugaban kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Yan Majalisar Dokokin Kasashen Iran Da Iraki Sun Amince Da Ra’yin Ficewar Sojojin Amurka Daga Iraki

Yan majalisar dokokin kasar Iran sun bukaci majalisar dokokin kasar Iraki su kori sojojin Amurka daga kasar ta Iraki.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran yana cewa, yan majalisar dokokin kasar Iran sun bayyana haka ne a lokacin ganawasu da wani dan majalisar dokokin kasar  Iraki mai wakiltan lardin Karbalar Imam Hussain (a) a majalisar dokokin kasar.

Labarin ya nakalto wakilin lardin Karbala a majalisar dokokin kasar Iraki yana cewa kasashen Iran da Iraki da gwamnatin kasar Iraki sun gamu a wannan ra’ayin kuma nan gaba abinda za’a yi Kenan. Yace dole ne sojojin Amurka su fice daga kasar Iraki, su kuma fice daga dukkan kasasjen larabawa a yankin. Ya ce da haka ne kasashen yankin zasu tabbatar da tsaron yankinsu.

Ebrahim Rezae dan majalisar dokokin kasar Iran ya bayyana cewa, kasar Amurka baa bin Amincewa ne, kuma shirin HKI na fadada mamayar karin yankunan kasashen larabawa na tafiya ne tare da umurnin Amurka kai tsaye.

A ranar 3 ga watan Jenerun Shekara ta 2020 ne shugaban Donal Trump ya bada umurnin kashe babban kwamandan rundunar Qudus ta Iran Janar Shahid Qasim Sulaimani a lokacinda ya shigo kasar Iraki daga Siriya tare da gayyatar gwamnatin kasar ta Iraki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DR Congo: M23 Ta Yi Barazanar Kauracewa Sulhu da Gwamnatin Kongo
  • Shugaban Kasar Ukraine Ya Nuna Sha’awar Ganawa Da Shugaban Kasar Rasha
  • Iran Ta Cilla Tauraron Dan’adam Mai Suna Nahid-2 A Yau
  • Faransa Zata Bayyana Amincewa Da Samuwar kasar falasdinu
  • An kashe mata da yara a sabon harin Filato
  • Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar
  • Iran: Iran Tana Cikin Kasashe Biyar Na Duniya Da Suka Ci Gaba Wajen Kiwon Dabbobi
  • Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa
  • Yan Majalisar Dokokin Kasashen Iran Da Iraki Sun Amince Da Ra’yin Ficewar Sojojin Amurka Daga Iraki