Rasha Ta Sha Alwashin Mayar Wa Da Nato Martani Mai Tsanani Idan Ta Kai Ma Ta Hari
Published: 26th, July 2025 GMT
Mataimakin shugaban kasar Rasha Nikolai Patrushev ya bayyana cewa; duk wani hari da za a kai wa yankin Kalligrad to zai fuskanci mayar da martani mai tsananin gaske.
Mataimakin shugaban kasar ta Rasha ya kuma ce; A bisa akidar tsaro ta Rasha duk wani hari da za a kai mata, to zai sa kasar ta yi amfani da dukkanin makaman da take da su, domin mayar da martani akan abokan gaba, daga ciki har da makaman Nukiliya idan bukatar haka ta taso.
Nikolai Patrushev wanda kamfanin dillancin labarun Sputnik ya yi hira a shi, ya ce;yankin Kallingrad kasar Rasha ne, don haka duk wani hari da za a kai masa zai sa su yi amfani da dukkanin karfin da suke da shi, wajen mayar da martani, har da makaman Nukiliya.
Mataimakin shugaban kasar ta Rasha ta kuma ce; Rasha tana sane da Shirin da kasashen yammacin turai su ke da shi, irin wannan, don haka Rasha tana da makaman da take da bukatuwa da su, domin kare yankin na killingirad.
Nikolai Patrushev ya bayyana shugabanin kasashen yammacin na yanzu da cewa, daidai suke da ‘yan Nazi,don haka za su shiga kwandon sharar tarihi kamar yadda magabatansu ‘yan Nazi na baya su ka shiga.
A baya kadan ne dai kwamandan sojan Amurka a turai da Afirak janar Chiristopher Donaho ya bayyana cewa; Nato ta shirya yadda za ta raunana layin tsaron da Rasha take da shi a yankin Kallingrad, domin karfafa hanyoyin aiki tare a tsakanin kasashen Nato.
Shi kuwa mai Magana da yawun fadar shugaban kasar Rasha Dmity Viskov, ya ce; Fadar gwamnatin kasar tana daukar wannan barazanar da hatsari.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: shugaban kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Sin na kira ga Amurka, da ta gaggauta dakatar da shuka kiyayya, da haifar da tashin hankali, da rura wutar gaba a tekun kudancin kasar Sin, kana ta kyale a dawo da yanayin zaman lafiya da daidaito a yankin. Lin Jian, ya bayyana hakan ne yau Litinin, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, lokacin da aka yi masa tambaya kan batun.
Wasu rahotanni daga kafofin watsa labarai sun bayyana cewa, a baya bayan nan, sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio, ya fitar da sanarwa dake cewa Amurka na goyon bayan kasar Philippines, game da watsi da ta yi da tsare-tsaren kasar Sin na kafa yankin kare muhallin halittu a tsibirin Huangyan Dao.
Lin ya ce “Mun gabatar da kakkarfan korafi a yau, dangane da kuskuren da Amurka ta tafka. Tsibirin Huangyan Dao yankin kasar Sin ne tun fil azal”, kuma kafa yankin kare muhallin halittu a tsibirin na karkashin ikon mulkin kai na Sin, wanda hakan ke nufin yana bisa turba, ya dace da doka, bai kuma cancanci suka ba. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp