Aminiya:
2025-07-27@23:15:55 GMT

HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna

Published: 28th, July 2025 GMT

Aisha ta koma gidan mijinta, marigayi Muhammadu Buhari da ke Jihar Kaduna, bayan shafe kwanaki a Daura tana karɓar gaisuwa.

Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe, ce ta jagoranci tawagar gwamnatin jihar wajen tarbar Aisha a Filin Jirgin Sama na Kaduna a ranar Lahadi.

Tsohon shugaban jami’ar Kashere ya rasu a Abuja Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP

Daga cikin waɗanda suka tarbe ta akwai Shugabar Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Munira Suleiman Tanimu, da wasu manyan jami’an gwamnati.

Tarbar da aka yi mata ta nuna yadda jihar ke ci gaba da girmama tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da iyalinsa bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban ƙasar nan.

Bayan tarbar ta, Dakta Hadiza ta raka Aisha Buhari da iyalanta zuwa gidan marigayin.

Wannan ya nunacewar iyalan marigayin za su ci gaba da rayuwa a jihar, tare da ƙarfafa zumunci tsakanin gwamnatin jihar.

Dubban mutane na ci gaba da miƙa ta’aziyyarsu kan rasuwar tsohon shugaban wanda ya mulki Najeriya sau biyu.

 

Ga hotunan a ƙasa:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aisha Buhari rasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Na Kara Bullo Da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Bukata Ta Musamman

A kokarin ta na inganta jin dadin al’umma, Gwamnatin jihar Jigawa ta gudanar da aikin tantance masu bukata ta musamman 200 a yankin Karamar Hukumar Birnin Kudu.

A jawabin daya gabatar, shugaban Karamar Hukumar, Dr Builder Muhammad Uba ya godewa gwamnatin jihar bisa kula da jin dadin masu bukata ta musamman a yankin da ma jihar baki daya.

Dr. Builder Muhammad, yace a baya akwai masu bukata ta musamman mutum 61 da ke con gajiyar shirin a yankin amma a yanzu kuma gwamnatin jihar ta amince a kara 139 da za a zabo daga mazabu 11 na yankin.

Builder, wanda ya sami wakilcin Kansila mai kula da shirin walwalar jama’a na yankin, Alhaji Ahmed magaji Bashir, yace Karamar Hukumar za ta bada hadin kai domin samun nasarar shirin a yankin.

A cewar sa, an samu karin alawus na masu bukata ta musamman daga naira dubu 7 zuwa dubu 10.

Shi ma a nasa, jawabin, jami’in shirin na yankin, Mallam Mansir Dahiru yace suna tantance masu bukata ta musamma da suka cancanta domin amfana da shirin a Karamar Hukumar ta Birnin Kudu.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon shugaban jami’ar Kashere ya rasu a Abuja
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Dashen Itatuwa Na Bana
  • HOTUNA: Shugaban Gambiya ya kai wa iyalan Buhari ziyarar ta’aziyya a Daura
  • Duk da kashe jagororin ’yan bindiga, Turji na ci gaba da kai hare-hare
  • ALGON Ta Jihar Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da NUJ Don Inganta Kwarewar Aiki
  • Daruruwan Jama’a Sun Halarci Sallar Jana’izar Marigayi Sarkin Gusau
  • Jihar Jigawa Na Kara Bullo Da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Bukata Ta Musamman
  • HOTUNA: Yadda Kwankwaso ya karɓi ’yan APC zuwa NNPP a Kano
  • Yadda aka mayar da yaran da aka sace a Kano masu wanke-wanke a Kudu