A ranar Alhamis 24 ga watan nan ne aka tantance tare da amincewa da biranen kasar Sin guda tara a matsayin biranen dausayi na kasa da kasa, yayin bude taron bangarorin da suka kulla yarjejeniyar Ramsar kan filayen dausayi karo na 15 (COP15), da aka gudanar a birnin shakatawa na Victoria Falls na kasar Zimbabwe, inda hakan ya kara adadin wadannan biranen a kasar Sin zuwa 22.

Sabbin biranen tara da aka amince da su sun hada da Chongming na Shanghai, da Dali na lardin Yunnan, da Fuzhou na lardin Fujian, da Hangzhou na lardin Zhejiang, da Jiujiang na lardin Jiangxi, da birnin Lhasa na jihar Xizang mai cin gashin kanta, da Suzhou na lardin Jiangsu, da Wenzhou na lardin Zhejiang, da kuma Yueyang da ke lardin Hunan.

Magajin garin birnin Kasane na kasar Botswana, Johane Chenjekwa, ya yaba wa kasar Sin bisa yadda ta inganta aikin kiyaye filin dausayi, yana mai cewa, Afirka za ta iya cin gajiyar hadin gwiwa da kasar Sin wajen kula da filin dausayi.

Ya kara da cewa, “Za mu sa lura mu ga abun da za mu iya koya daga gare su yayin da muke hulda da juna. Su ma suna da muradin koyon yadda muke gudanar da abubuwa a nan, don haka ana samun babbar kwarewa idan ana cudanya da juna.” (Abdulrazaq Yahuza jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21 October 30, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
  • Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya