Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jaddada Aniyar Iran Ta Ci Gaba Da Inganta Sinadarin Uranium
Published: 25th, July 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Babu shakka Iran za ta ci gaba da inganta sinadarn Uranium
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana a jiya Alhamis dangane da tattaunawar da Iran za ta yi da kungiyar kasashen Turai da za a yi a yau Juma’a a birnin Istanbul na Turkiyya cewa; Za a ci gaba da inganta sinadarin Uranium a cikin kasar Iran, kuma kasar ba za ta yi watsi da wannan hakkin na al’ummar Iran ba.
A cikin bayanin da ya yi a gefen ziyarar da ya kai ga iyalan shahidan Laftanar Janar Baqiri, Araqchi ya kara da cewa; Ko da yaushe Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take ta ci gaba da shirinta na makamashin nukiliya na zaman lafiya bisa tsari mai ma’ana da inganci.
Ya kara da cewa: Iran ba ta taba yin kasa a gwiwa ba wajen samun amincewar kasashe da a wasu lokutan suke nuna damuwa, a maimakon haka, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta gabatar da bukatunta na mutunta hakkinta na amfani da makamashin nukiliya cikin lumana, ciki har da inganta harkokin makamashi.
Ya ci gaba da cewa: Tattaunawar da za a yi a gobe ci gaba ce ta wadancan shawarwarin da suka gabata, matsayar Iran a bayyane take, wajibi ne duniya ta san cewa ba a samu wani sauyi a matsayin kasar ba, kuma za ta himmatu wajen kare hakkin al’ummar Iran a fagen samar da makamashin nukiliya ta hanyar lumana, musamman batun inganta makamashin nukiliya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: makamashin nukiliya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamantin Kasar Siriya Ta Rufe Hanyoyin Shiga BirninSiweida Na Kasar Saboda Ci Gaba Da Bullar Rikici
Hukumomin rikon kwaryar Siriya sun rufe hanyoyin zuwa birnin Sweida bayan sake bullar wani tashin hankali
Dakarun gwamnatin Siriya na ci gaba da rufe hanyoyin da ke shiga lardin Sweida da ke kudancin kasar tun daga wayewar garin ranar Asabar, bayan kazamin fadan da aka gwabza tsakanin kabilar Bedouin da mayakan Duruz a cikin birnin. A halin da ake ciki, ana ci gaba da kokarin da ake yi na cikin gida da waje na wanzar da tsagaita bude wuta da kare fararen hula.
Ana zaman dar dar a lardin Suwayda da ke kudu maso yammacin kasar Siriya, inda dakarun gwamnati ke ci gaba da rufe hanyoyin da ke shiga lardin tun da safiyar Asabar, bayan kazamin fadan da aka gwabza tsakanin ‘yan kabilar Bedouin da mayakan Duruz a cikin birnin.
Hukumomin rikon kwaryar Siriya sun samu nasarar kwace iko da lardin, tare da kafa shingaye na kasa domin raba bangarorin da ke fada da juna bayan rattaba hannu kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta. Sun kuma hana wucewar daidaikun mutane da ayarin motocin sojoji a kusa da lardin.