Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jaddada Aniyar Iran Ta Ci Gaba Da Inganta Sinadarin Uranium
Published: 25th, July 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Babu shakka Iran za ta ci gaba da inganta sinadarn Uranium
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana a jiya Alhamis dangane da tattaunawar da Iran za ta yi da kungiyar kasashen Turai da za a yi a yau Juma’a a birnin Istanbul na Turkiyya cewa; Za a ci gaba da inganta sinadarin Uranium a cikin kasar Iran, kuma kasar ba za ta yi watsi da wannan hakkin na al’ummar Iran ba.
A cikin bayanin da ya yi a gefen ziyarar da ya kai ga iyalan shahidan Laftanar Janar Baqiri, Araqchi ya kara da cewa; Ko da yaushe Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take ta ci gaba da shirinta na makamashin nukiliya na zaman lafiya bisa tsari mai ma’ana da inganci.
Ya kara da cewa: Iran ba ta taba yin kasa a gwiwa ba wajen samun amincewar kasashe da a wasu lokutan suke nuna damuwa, a maimakon haka, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta gabatar da bukatunta na mutunta hakkinta na amfani da makamashin nukiliya cikin lumana, ciki har da inganta harkokin makamashi.
Ya ci gaba da cewa: Tattaunawar da za a yi a gobe ci gaba ce ta wadancan shawarwarin da suka gabata, matsayar Iran a bayyane take, wajibi ne duniya ta san cewa ba a samu wani sauyi a matsayin kasar ba, kuma za ta himmatu wajen kare hakkin al’ummar Iran a fagen samar da makamashin nukiliya ta hanyar lumana, musamman batun inganta makamashin nukiliya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: makamashin nukiliya
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.
Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA