HausaTv:
2025-07-27@03:40:20 GMT

Jagora: Za’a Gaggauta Ci Gaba A Ilmi Da Fasahar Tsaron Sojojin Kasar

Published: 26th, July 2025 GMT

Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana cewa JMI zata gaggauta ci gaba a fasahar tsaron kasa da kuma fasahar zamani a dukkan fagage bayan yakin kwanaki 12 da HKI da Amurka.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jagoran yana fadar haka a cikar kwanaki 40 da shahadar manya-manyan kwamandojin sojojin kasar da kuma masana fasahar Nukliya a kasar.

Jagoran ya kara da cewa dukkan ilmomi tsaron kasa da kuma fasaha za su cilla da saura don samun ci  gaba.  A sakon da jagoran ya aikawa mutanen kasar ya yi tir da hare-haren da HKI da kuma Amurka suka kaiwa kasar Iran, sannan yay aba da sojojin kasar Iran kan duka mai karfin da suka yiwa makiya.

Yace: Babu shakka an yi rashin manya-manyan kwamandojin sojojin kasar Kamar Bakiri salami, Rashid Hajizadeh shadmani da sauransu, abun yayi mana nauyi, hakama mun rasa masana fasahar Nukliya Tehranchi da Abbasi, amma kuma muna godiyar All..makiya basu cimma mummunan manufofinsu a kan Iran ba.  Yace: Manufar HKI na maida kasar Iran baya ya kasa kaiwa ga nasara,.  A ranar Jumma’a 13 ga watan yunin da ya gabata ne jiragen yakin HKI suka kai hare-hare a wurare da dama a cikin nan birnin Tehran. Inda suka kai wadannan manya-manyan mutane ga shahada. Sannan kafin kasar Yakin wanda suka nemi a tsaida shi sun dauki darasi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 An Jikkata  Sojojin Sahayoniya 9 Ta Hanyar Take Su Da Mota

Kafafen watsa labarun HKI sun ce wani mutum a cikin motar da yake tukawa ya nufi kan ‘yan sahayoniya a mahadar “Hahsrun” a kusa da “Kafar-Yona”dake yammacin Tul-Karam.

Bayan da matumin ya take ‘yan sahayoniyar ya fice daga yankin ba tare an iya tsayar da shi ba.

Majiyar ta kara da cewa; 9 daga cikin ‘yan sahayoniyar da su ka jikkata sojoji ne.

Tashar talabijin din ta 12: ta ambaci cewa; Wanda ya take sojojin ya iya gudu daga wurin, ba tare da an tsayar da shi ba.

Ita kuwa jaridar ‘ Yasrael Home” ta bayyana cewa; An baza ‘yan sanda a wurin da aka kai hari, domin gano inda maharin yake.

Kungiyoyin Falasdinawa sun yi maraba da wannan harin, tare da yin kira a ci gaba da gudanar da irinsa da yawa.

Kungiyar Hamas ta ce, dole a tsammaci wannan irin harin, bisa la’akari da laifukan da HKI take tafkawa a Gaza da yammacin kogin Jordan.

Kungiyar Jihadul-Islami kuwa cewa ta yi, hari irin wannan yana kara tabbatar da yadda al’ummar Falasdinu ta sha alwashin ci gaba da riko da kasarta da kuma kalubalantar ‘yan mamaya da dukkanin abinda su ka mallaka.

Shi kuwa kwamitin gwagwarmaya na Falasdinu ta yi kira ne ga dukkanin  Falasdinawa da su yunkura domin fada da sojojin sahayoniya.

Ita kuwa kungiyar “Mujahidun-al-Falasdiniyya ta sa wa harin albarka tare da bayyana shi a matsayin babban sako ga ‘yan mamaya dake cewa martani akan kisan gillar da suke yi zai fadada.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 6 Ne Suka Yi Shahada Sanadiyyar Hare-haren Yan Ta’adda A Zahidan
  • Duk da kashe jagororin ’yan bindiga, Turji na ci gaba da kai hare-hare
  • Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jaddada Aniyar Iran Ta Ci Gaba Da Inganta Sinadarin Uranium
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: Taro Tsakanin Iran Da Tawagar Kasashen Turai Dama Ce Ta Gyarar Tunanin Tarai
  •  An Jikkata  Sojojin Sahayoniya 9 Ta Hanyar Take Su Da Mota
  • Ayatullahi Makarem Shirazi Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Hadin kai Da Suka Bayar Lokacin Yakin Kwanaki 12
  • Yan Majalisar Dokokin Kasashen Iran Da Iraki Sun Amince Da Ra’yin Ficewar Sojojin Amurka Daga Iraki
  • Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno