Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
Published: 25th, July 2025 GMT
Da yammacin yau Alhamis ne firaministan kasar Sin Li Qiang, ya shugabanci taron tattaunawa tsakanin shugabannin Sin da EU karo na 25, tare da shugaban majalisar EU Antonio Costa, da shugabar hukumar EU Ursula von der Leyen a nan birnin Beijing.
A yayin taron, Li Qiang ya bayyana cewa, Sin da EU suna da moriya iri daya wadda babu rikici a cikinta.
Li Qiang ya ce, kamata ya yi bangarorin biyu su kara yin hadin gwiwa, da tabbatar da ra’ayin cudanyar bangarori daban daban, da gudanar da ciniki cikin ‘yanci, don tabbatar da adalci da odar tattalin arziki, da cinikayya a duniya baki daya.
A nasu bangare, Antonio Costa da Ursula von der Leyen, sun bayyana cewa, bangaren EU yana fatan yin kokari wajen zurfafa dangantakar abokantaka a tsakaninsa da kasar Sin a dogon lokaci, da kara yaukaka mu’amala da juna, da fahimtar juna, da mai da hankali ga batutuwan da suke mayar da hankali a kansu, da sa kaimi ga hadin gwiwarsu a fannonin cinikayya da zuba jari, da kokari tare wajen tinkarar kalubalen duniya, da nuna goyon baya ga hukumar WTO, ta yadda za ta taka muhimmiyar rawar raya dangantakar tattalin arziki, da cinikayya a tsakanin sassan kasa da kasa, da kuma tabbatar da ra’ayin cudanyar bangarori daban daban. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung
A wannan rana, a gun taron manema labarai da aka gudanar bayan kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC, Lee Jae-myung ya ce hadin gwiwar tattalin arziki tsakanin Sin da Koriya ta Kudu yana da matukar muhimmanci, ya kuma yi imanin cewa birnin Shenzhen na kasar Sin zai karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC cikin nasara a shekara mai zuwa.(Safiyah Ma)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA