Aminiya:
2025-11-03@00:56:30 GMT

Matashi ya tono gawar kakarsa don yin tsafin kuɗi da ƙoƙon kanta

Published: 26th, July 2025 GMT

An kama wani matashi da ake zargi da tono gawar kakarsa ta ɓangaren uwa tare da sare kanta da nufin yin tsafin kuɗi a Jihar Naje.

Rundunar ’yan sandan Jihar Neja ta kama mutumin mai shekaru 31 ne bayan dubansa ta cika a yankin.

Kakakin rundunar, Wasiu Abiodun, ya cewa wanda ake zargin tare da abokansa da suka taimaka masa ya tabbatar musu cewa zai yi tsafin kudi ne da ƙwarangwal din tsohuwar.

A cewar kakakin rundunar wanda ake zargin ya furta cewa yana neman tsafin ne don biyan bashin da ya kai sama da Naira miliyan biyu.

Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji Sojoji sun ceto yaro da aka sayar shekaru 3 a Filato

A ranar 19 ga Yuli, 2025 ne jami’an ’yan sanda suka kama wannan gungun mutane da kai a otel ɗin Bida.

Babban wanda ake zargin ya tabbatar cewa kan kakarsa ce mai shekaru sama da 90 a lokacin da ta rasu kimanin shekaru biyu da suka gabata.

Ya ce da farko ya samo kan ne bisa umarnin wani boka, don neman kuɗi cikin hanzari. Amma, bayan jin sharuddan tsafin, ya kasa bi, sai ya ɓoye kan na tsawon shekaru biyu.

Daga baya, abokinsa da wani kuma sun yi masa tayin sayenkan a kan Naira 100,000, kuma suka biya Naira 40,000 a matsayin kuɗin kafin alƙalami.

Daga nan suka kai wani wanda ake zargi da ninka kuɗi, da ya nemi Naira 500,000 don yin tsafin kuma sun biya shi da kaɗan-kaɗan.

Bayan an gama aikin, ya umarce su kada su buɗe ganga har sai ya gaya musu.

Makonni sun shude babu labari ko kuɗi sai suka yi masa takakkiya zuwa gidansa, amma ya shawo kansu cewa su haɗu a wani otel a Bida inda za su karɓi kuɗinsu.

A otel din ne kuma ’yan sanda suka kama su gaba ɗayansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Gawa ƙasarsa Tsohuwa zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure

Babbar Kotun Kano mai lamba 7 da ke zama a cikin birni ta bayar da umarnin tsare Aminu Ismail, mazaunin Unguwar Bai a Karamar Hukumar Ajingi ta jihar, bisa zarginsa da kashe mahaifinsa, Malam Dahiru Ahmad, ta hanyar caka masa wuƙa har lahira.

Lamarin ya faru ne bayan samun sabani tsakaninsu kan aniyar Aminu ta ƙara aure, wadda mahaifinsa ya ƙi goyon baya saboda abin da ya kira halin tattalin arzikin da ake fama da shi a kasa.

Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum

A cewar lauyan masu ƙara, Barrista Lamido Abba Sorondinki, wanda ake tuhuma ya shaida wa mahaifinsa niyyarsa ta kara mata ta biyu, amma mahaifinsa ya ba shi shawarar kada ya yi hakan, yana mai danganta matsalar da halin tattalin arzikin ƙasa ke ciki.

Wannan sabani ya rikide zuwa faɗa, inda ake zargin Aminu da caccaka wa mahaifin nasa wuƙa a ƙirji, lamarin da ya jawo masa rauni mai tsanani har ya rasa ransa.

An gurfanar da Aminu da laifin kisan kai, wanda ya saba da Sashe na 221 na kundin penal code.

Ana ci gaba da shari’ar, kuma kotu ta bayar da umarnin tsare shi har zuwa lokacin da za a ci gaba da sauraron ƙarar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure