Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar Dokokin jihar Jigawa, Alhaji Aminu Zakari, ya bayyana cewa gudanar da ayyukan raya kasa sosai a yankunan karkara zai kara daga martabar jihar a idon sauran jihohin kasar nan.

Ya yi wannan tsokaci ne yayin ziyarar aiki a sakatariyar karamar hukumar Dutse, inda ya ja hankalin shugaban karamar hukumar game da bukatar bada fifiko ga bangaren ayyukan raya kasa fiye da harkokin yau da kullum domin karfafa matakin cigaban karamar hukumar.

A cewar sa, kwamatin na rangadin kananan hukumomin jihar 27 ne domin bibiyar yadda ake aiwatar da tanade tanaden kasafin kudi domin tabbatar da kashe kudaden gwamnati ta hanyar da ta dace, Inda Kwamatin ke duba kundin bayanan sha’anin mulki da na harkokin Kudi da nufin cusa dabi’ar aiki da tanade tanaden aikin gwamnatin da ka’idojin kashe kudade.

Kazalika, Alhaji Aminu Zakari yace an kafa kananan kwamitoci guda 2 domin ziyarar gani da ido kan ayyukan raya kasa da karamar hukumar Dutse ta gudanar ga jama’ar yankin.

Karamin Kwamati na daya bisa jagorancin wakilin mazabar
Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashim Kanya, ya duba aikin ginin Masallacin khamsissalawati na garin Barangu da rumfunan kasuwa a garin ‘Yar Gaba da Masallacin khamsissalawati na Gidan Gawo da aikin ginin karamin asibitin garin Charka da aikin karamin asibitin Zangon Buji, da aikin gyaran Masallacin Juma’a na garuruwan Kacha da Barandau.

Shi kuwa karamin kwamati na 2 bisa jagorancin wakilin mazabar Buji, Alhaji Sale Baba Buji ya duba aikin hanyar Burji daga Bolari ta wuce Bakin Jeji zuwa Katangar lafiya, akan naira milyan 129 wadda wani kamfani ya yi, sai kuma rumfar kasuwa a garin Hammayayi da sanya fitilu masu amfani da hasken rana makaranta sikandire ta garin Madobi da Masallacin Juma’a na garin Baranda.

A jawabin sa na maraba, shugaban karamar hukumar Dutse Malam Sibu Abdullahi, ya bayyana ayyukan Kwamatin a matsayin ginshikin samun nasarar gudanar da mulkin kananan hukumomi.

Ya bayyana kudurin sa na karbar gyare-gyare da shawarwarin Kwamatin domin cigaban karamar hukumar sa.

Malam Sibu Abdullahi ya bayyana kudurinsa na hada Kai da majalisar Dokokin jihar Jigawa domin shiryawa kansiloli da Akawun majalisar kamsilolin bita game da tsare tsaren zaman majalisa kamar yadda mataimakin sakataren Kwamatin Malam Sadiq Muhammad ya kawo shawara.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa karamar hukumar Dutse

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala

Hukumar Tace Fina-Finai da Dab’i ta Jihar Kano ta haramta shirya duk wata muƙabala tsakanin mawaƙan yabon Annabi (S.A.W), tare da gayyatar mawaƙa Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi su bayyana a gabanta.

Hukumar ta kuma gayyaci mawaƙan ne tare da sauran waɗanda suka jagoranci muƙabalar da fitattun mawaƙan biyu suka yi ranar Litinin, da su bayyana a gabanta cikin sa’o’i 24.

Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu

Hakan na zuwa ne ƙasa da kwana ɗaya bayan ɓullar wata muhawara da aka yi tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi kuma ta karade shafukan sada zumunta, wacce hukumar ta bayyana a matsayin karya dokokin aikinta.

Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da hakan ranar Talata, inda ya ce ɗaukar matakin wani yunƙuri ne na tabbatar da zaman lafiya, daidaito da bin doka tsakanin mawaƙan nishaɗi da na addini.

El-Mustapha, a cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar, ya kuma ce an haramta duk wata nau’in muƙabala daga mawaƙan addini a jihar ba tare da izinin hukumar ba.

A yayin da yake ƙaddamar da wani kwamitin bincike da shugaban hukumar ya naɗa karkashin Daraktan Ayyuka na Musamman a hukumar, Isah Abdullahi, El-Mustapha ya umarci waɗanda aka gayyatar da su bayyana a gaban kwamitin domin amsa tambayoyi.

Hukumar ta ce shirya irin waɗannan muhawara ba tare da izininta ba ya saɓa doka kuma zai iya jawo hukunci mai tsanani ga wanda suka karya.

Hukumar ta kuma jaddada ƙudirinta na ci gaba da kula da ayyukan mawaƙan da masu nishaɗantarwa a faɗin jihar tare da yin kira ga jama’a da su zauna lafiya sannan su ci gaba da ba ta haɗin kai a ayyukanta.

Yadda aka yi muƙabala tsakanin Shehi Tajul Izzi da Maidubun Isa

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar