HausaTv:
2025-07-27@20:01:11 GMT

Iran Da Afganistan Sun Tattauna Dangane Da Komawar Afganawa Gida

Published: 27th, July 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya zanta ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Afganistan Amir Khan Muttaki a yau Lahadi inda bangarorin biyu suka tattauna dangantaka tsakanin kasashen biyu da kuma al-amuran yankin wadanda suka hada da batun gaza da kuma halin da take ciki.

Kamfanin dillancin labaran Tasnima na kasar Iran ya nakalto ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi yana cewa kasar Iran ta kira taron gaggabawa na kungiyar OIC ta kasashen musulmi don tattauna wannan batun.

A nashi bangaren muttaki ya bukaci gwamnatin kasar Iran ta maida yan kasar Afganistan wadanda suke zauna a kasar zuwa gida tare da mutuntasu. Kafin haka dai a lokacin yakin kwanaki 12 tsakanin HKI da Iran jami’an tsaro a kasar Iran sun kama yan Afganistan da dama suna aikiwa HKI don dan kudade da suke samu

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Bakaken Fatar Amruka Da Suke Yin Hijira Zuwa Afirka  Suna Karuwa

Ana samun Karin bakaken fatar Amurka da suke baro kasar suna dawo wa nahiyar Afirka domin samun kyakkyawar rayuwa a cikinta.

Mafi yawancin bakaken fatar suna nuna rashin gamsuwarsu da yanayin tattalin arziki da kuma siyasa na Amukra da su ka taka rawa wajen sa su, daukar matakin komawa Afirka da can ne asalin kakanninsu.

Wani dan kasar Amurka da ya rika yawo a tsakanin kasashe mabanbanta na Afirka a karshe ya tare a kasar Kenya, ya bayyana yadda yake jin ya saje a cikin nahiyar Afirka fiye da a can Amurka.

Auston Holleman wanda ya shahara da wallafa sakwanni a You Tube ya kara da cewa; Dukkanin mutane a Afirka sun yi kama da juna, ba  kamar acikin turai, ko yankin Latin ba. “

Holleman ya kuma bayyana cewa yanayin siyasar Amruka a halin yanzu ya sa kasar tana fada da duk duniya baki daya.

Tun a 2019 ne dai kasar Ghana ta kaddamar da wani shiri na jawo hankalin bakaken fata a ko’ina suke a duniya domin samun wurin zama a cikinta.

A shekarar 2024 Ghana din ta ba da izinin zaman ‘yan kasa ga bakaken fata 524,mafi yawancinsu daga kasar Amurka.

Tun bayan da  kamfanonin bakaken fata  na Amurka irin su  Adilah su ka koma Ghana, an sami karuwar bakaken fatar da suke komawa can.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yanke Hukuncin Kisa Kan Yan MKO A Nan Iran
  • IRGC Ta Ja Kunnen Kasashen Turai Dangane Da Taimakon Da Suke Bawa HKI
  • Bakaken Fatar Amruka Da Suke Yin Hijira Zuwa Afirka  Suna Karuwa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kiran Cewa; Ina Masu Fafatukar Kare Hakkin Dan Adam Suke A Bala’in Gaza?
  • Kasar Iran Ta Ce Tana Hulda Da Amurka Ta Hanyar Masu Shiga Tsakani
  • An Watse A Taron EU Da China Saboda Ricikin Kasuwanci Da Siyasa  Tsakaninsu
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jaddada Aniyar Iran Ta Ci Gaba Da Inganta Sinadarin Uranium
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: Taro Tsakanin Iran Da Tawagar Kasashen Turai Dama Ce Ta Gyarar Tunanin Tarai
  • IMF na Shirin aikewa da wata tawaga zuwa Senegal domin tattauna batun basussukan kaaar