Gwamnatin Yobe ta bada tallafi ga iyalan ’yan banga da suka rasu
Published: 24th, July 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Yobe ta raba tallafin kuɗi ga iyalan ’yan banga da suka rasa rayukansu da kuma waɗanda suka samu raunuka a bakin aiki.
Kuɗaɗen wanda Daraktan ayyuka na musamman, Muhammad Alhaji Baba ya miƙa a madadin sakataren gwamnatin jihar sakamakon umarnin da Gwamna Mai Mala Buni ya bayar na a yi hakan.
Wannan shiri dai wani ɓangare ne na shirin jin daɗin jama’a na jaha ga jami’an tsaro domin tabbatar da cewa, iyalan ’yan banga da abin ya shafa sun samu tallafi.
A ƙarƙashin shirin, kowane dangin ɗan banga da ya rasu ya karɓi Naira dubu ɗari ₦500, yayin da waɗanda suka jikkata an ba su Naira dubu ɗari ₦200 kowanne.
Da yake jawabi a lokacin rabon kuɗaɗen, Daraktan ya jaddada ƙudirin gwamnatin jihar na haɗa kai da duk masu ruwa da tsaki a harkar tsaro da suka haɗa da ƙungiyoyin ‘yan banga domin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da aka samu a Jihar Yobe.
Ya jajantawa iyalan waɗanda suka rasu, ya kuma yaba da jajircewa, sadaukarwa da ‘yan bangar suka yi wajen tabbatar da tsaron jihar.
“Jarumtar da kuke nunawa lalle kuna yinta bisa ƙa’Ida, kuma jin daɗin ku ya kasance babban fifiko ga wannan gwamnati,” in ji shi.
Tallafin kuɗin wani ɓangare ne na ƙoƙarin da ake yi na ƙarfafa tsarin tsaron al’umma da kuma ba da agaji ga waɗanda abin ya shafa a yaƙin da ake yi da masu tayar da ƙayar baya.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Yobe
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON Ta Jihar Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da NUJ Don Inganta Kwarewar Aiki
Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomi ta Jihar Jigawa (ALGON) ta yi alkawarin kafa kyakkyawar haɗin gwiwa da ƙungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ) reshen jihar, domin inganta ƙwarewar jami’an hulɗa da jama’a a fadin jihar.
Shugaban ALGON, Farfesa Abdurrahman Salim ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi shugabannin NUJ a wata ziyarar girmamawa da suka kai masa a sakatariyar ALGON da ke Dutse, babban birnin jihar.
Farfesa Salim ya jaddada muhimmancin yada bayanai a harkokin mulki da kuma isar da ayyuka ga jama’a, yana mai cewa samun ingantacciyar sadarwa na da matuƙar muhimmanci.
A cewarsa, bai wa jami’an hulɗa da jama’a horo da ƙwarewa zai taimaka wajen sauƙaƙe isar da sahihan bayanai ga al’umma.
Farfesa Salim ya tabbatar wa NUJ da cikakken goyon baya da haɗin gwiwar ALGON wajen ƙarfafa ƙwarewar jami’an bayanai, domin su daidaita da sauye-sauyen da ke faruwa a duniyar kafafen yaɗa labarai.
Tun da farko, Shugaban NUJ na jihar Jigawa, Kwamared Isma’il Ibrahim Dutse, ya ce shugabannin ƙungiyar sun kai ziyarar ne domin neman haɗin kai da goyon baya daga ALGON.
Ya ce NUJ ta yi amanna cewa sadar da bayanai na da matukar muhimmanci wajen tafiyar da mulki da kuma isar da ayyuka ga jama’a.
Usman Mohammed Zaria