Kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Human Right Watch” ta yi kira ga gwamnatin sojan jamhuriyar Nijar da ta saki tsohon shugaban kasar Muhamad Bazum, wanda ake tsare da shi tun lokacin juyin mulkin watan Yuli na 2023.

Kungiyar ta kuma ce, ci gaba da tsare Muhammad Bazum da ake yi ba tare da yi masa shari’a ba, ya sabawa doka da kuma take dokokin kasa da kasa na sharia.

 Bayan juyin mulkin na 2023, shugabannin soja sun yi alkawalin gabatar da Bazum a gaban kotu domin yi masa shari’a bisa zargin cin amanar aksa.

A 2024, kotun musamman da aka kafa ta cirewa tsohon shugaban kasar rigar kariya, da hakan ya zama tamkar share fage domin yi masa sharia,sai dai har yanzu hakna ba ta faru ba.

Lauyoyin da suke bai wa Bazzoum kariya sun nemi taimakon kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada MDD da kungiyar tattalin arziki ta yammacin Afirka ( ECOWAS).

Dukkanin kungiyoyin na kasa da kasa da kuma na yammacin Afirka sun sha yin kira da a saki Bazzum ba tare da wani sharadi ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Zargi Amurka Da HKI Da Wargaza Dokokin Kasa Da Kasa Da Kuma Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa

Wani babban Jami’in diblomasiyyar kasar Iran ya zargi Amurka da kuam HKI da laifin Zagon kasa ga dokokin kasa da kasa da kuma sabawa yarjeniyoyi da dokokin MDD.

Kazen Gharibabadi mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan al-amuran sharia na kasa da kasa yana fadar haka a jiya Laraba a majalisar dinkin duniya a birnin NewYork na kasar Amurka, a lokacinda yake jawabi a gaban kwamitin tsaro na MDD dangane da kasar Falasdinu.  

Gharibabadi ya bayyana cewa, Amurka da HKI sune manya-manyan masu haddasa rashin tsaro a kasashen yankin Asiya ta yamma.

Jami’in diblomasiyyar ya bayyana cewa Amurka da HKI ne suke haddasa halin da ake ciki a Gaza, na yuwan da kuma kisan kiyashi a Gaza da kashesu hanyar daukar yunwa a matsayin makami. Hakama tashe-tashen hankula a kasashen Yemen, Siriya da kuam Lebanon.

Banda haka wadanan kasashen biyu ne suka haddasa yakin kwanaki 12 a kan kasar Iran a cikin watan Yunin da ya gabata.

Yace wadan nan kasashe ne suke haddasa matsaloli da ruda gidajen falasdinawa a yankin yamma da kogin Jordan, Yace HKI ta kori miliyoyin Falasdinawa daga gidajensu ta maidasu yan gudun hijira a kasashe makobta da kuma da sauran kasashen duniya,

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
  • 2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku
  • Hukumar Ba Da Agajin Jin Kai Ta ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinawa Ta “UNRWA” Ta Sanar Da Kashe Ma’aikatan 330 A Gaza
  • ‘Yan Tawayen Sudan Ta Kungiyar Rapid Support Forces Sun Kashe Mutane 27 A Yammacin Jihar Kordofan Ta Kasar Sudan
  • Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Ruwa da iska sun kashe mutum, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Asusun Kula Da Kananan Yara Na Majalisar Dinkin Duniya “UNICEF” Ya Yi Gargadi Kan Bala’in Jin Kai A Gaza
  • Iran Ta Zargi Amurka Da HKI Da Wargaza Dokokin Kasa Da Kasa Da Kuma Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa
  • Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya