A yayin da ‘yan sandan ke gudanar da bincike a yankin, rahotanni sun ce jami’an sun gano wata mata ‘yar Nijeriya a Coach A-2, Seat No. 27, tare da wani yaro da wata jakar balaguro kala-kala.

Rahoton ya bayyana cewa bayan an yi mata tambayoyi, ta bayyana sunanta Doris daga Nijeriya kuma ta ce yaron da ke tare da ita, wanda ta bayyana sunansa Miracle, nata ne.

RPF ta lura cewa “da aka yi mata tambayoyi a gaban shaidu masu zaman kansu, matar ta amsa cewa tana dauke da kayan maye.”

Daga baya an kai ta zuwa gidan RPF a Panbel domin cikakken bincike.

Rahoton ya lura cewa a cikin jakar balaguron, jami’an sun gano bakaken fakiti guda biyu da aka lullube da kayan roba da aka yi wa lakabi da “BINTAGE.”

A cewar ‘yansanda, na’urorin gwajin muggan kwayoyi daga baya sun tabbatar da cewa abin da ke ciki hodar iblis ce mai nauyin kilogiram 2.002.

Binciken da aka yi a baya ya gano wata jakar Mickey Mouse mai ja-da-shudi ta yara da ta boye a cikin babbar jakar.

‘Yansandan sun bayyana cewa karamar jakar na dauke da fakitin takardu guda biyu – daya mai lakabin “Kellogg’s Corn Flakes” da sauran “Bongchi Perfect Roll.”

An samu rahoton cewa wadannan suna dauke da fararen sinadarai na crystalline, daga baya aka gano su da methamphetamine, mai nauyin kilogiram 1.488.

Hukumomin CR sun tabbatar da cewa “magungunan da aka kama, darajarsu ta kai kusan Rs 36 crore”

Etumudon ta zama mace ta biyu ‘yar Nijeriya da aka kama a Indiya cikin kasa da watanni biyu bisa laifin safarar muggan kwayoyi.

Ta bi sahun wasu ‘yan Nijeriya da dama da a halin yanzu ke fuskantar shari’a a kasar kan irin wadannan laifuka.

“Aikin da aka gudanar cikin bayanan sirri, an kaddamar da shi ne da hadin gwiwa kuma an gudanar da bincike a kan isowar jirgin a Platform No. 7, Panbel Railway Station,” in ji jami’an CR.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato

Gobir ya bayyana cewa kowanne daga cikin waɗanda aka ceto zai samu Naira 100,000, buhun gero ɗaya da buhun masara ɗaya a matsayin tallafi.

Shi ma da yake magana, Shugaban ƙaramar hukumar Isa, Alhaji Sherifu Abubakar Kamarawa, ya gode wa gwamnatin jihar bisa taimakon da ta bayar, yana mai cewa hakan ya nuna damuwar gwamnati kan tsaron rayuka da jin daɗin al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu  A Kaduna
  • WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
  •   New York Times: Harin A Sansanin Udaidai Ya Jaza Wa Amurka Asarar Dala Miliyan 111
  • NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159
  • Wani mutum ya buɗe Ofishin Jakadancin Indiya na bogi a ƙasar
  • ‘Yan Tawayen Sudan Ta Kungiyar Rapid Support Forces Sun Kashe Mutane 27 A Yammacin Jihar Kordofan Ta Kasar Sudan
  • ‘Yan Nijeriya Miliyan 40 Ke Fuskantar Barazanar Kwararowar Hamada – Ministan Muhalli
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato
  • Tinubu ya sake miƙa buƙatar karɓo bashin Dala miliyan 347 daga ƙetare