Aminiya:
2025-07-27@06:00:15 GMT

Super Falcons sun lashe gasar WAFCON karo na 10 bayan doke Maroko

Published: 27th, July 2025 GMT

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta mata ta Najeriya, Super Falcons, ta sake kafa tarihi bayan ta doke ƙasar Maroko da ci 3–2 a wasan ƙarshe na gasar WAFCON.

Yanzu haka Super Falcons ta lashe kofin karo na 10, wanda shi ne adadi mafi yawa da wata ƙasa ta taɓa lashewa a tarihin gasar.

ADC ce kaɗai za ta iya magance matsalolin Arewa — David Mark Dole gyaran kundin tsarin mulki ya haɗa kan ƙasa da shugabanci na gari — Abba

Maroko ce ta fara jefa ƙwallaye biyu cikin mintuna 25 ta hannun Ghizlane Chebbak da Sanaa Mssoudy, lamarin da ya tayar da hankalin magoya bayan Super Falcons a filin wasa na Rabat.

Amma Najeriya ba ta karaya ba.

A minti na 64, Esther Okoronkwo ta warware ƙwallo a bugun fenariti, sannan ta taimaka wajen cin ƙwallo ta biyu da Folashade Ijamilusi ta jefa a minti na 71.

Saura minti biyu a tashin daga wasan, Jennifer Echegini ta ci ƙwallo ta uku, wanda hakan ya sa ta girgiza duniyar ƙwallo.

Wannan nasara ta tabbatar da mamayar da Super Falcons ta yi a Afirka.

Ƙungiyar ta lashe dukkanin wasanim ƙarshe da ta buga a gasar WAFCON, kuma yanzu tana da kofuna 10 a tarihin gasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ƙwallo Maroko Najeriya WAFCON

এছাড়াও পড়ুন:

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Ya ce tituna a Arewa sun lalace kuma gwamnati tana nuna rashin kulawa ga yankin. “Jiya da jirgi zan biyo na taho, amma aka ɗage jirgi daga ƙarfe 3 na yamma zuwa 8 na dare, sai na taho ta mota. Daga Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano abin takaici ne. Wannan aikin titi tun lokacin farkon hawa gwamnatin APC ake yinsa.”

Kwankwaso ya kara da cewa ana gudanar da manyan ayyuka a Kudu cikin hanzari, amma an bar ayyuka masu mahimmanci a Arewa babu kulawa.

“Muna jin ana gina titi daga Kudu zuwa Gabas. Muna maraba da ci gaba a ko’ina a Nijeriya. Amma gwamnati tana ɗaukar duk arzikin ƙasa ta zuba a ɓangare ɗaya kaɗai, ba ta yin aiki da ra’ayin ‘yan ƙasa gaba ɗaya,” cewarKwankwaso.

Ya roƙi gwamnatin Tinubu da ta sake duba tsarin rabon arziki tare da tabbatar da yin adalci a dukkan yankuna.

“Lokaci ya yi da gwamnati za ta sauya, ta tabbatar wa da ’yan Nijeriya cewa gwamnati ce ta ƙasa gaba ɗaya, ba ta wani ɓangare kawai ba,” in ji Kwankwaso.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Super Falcons ta lashe gasar WAFCON karo na 10 bayan doke Maroko
  • Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
  • Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Na Mata 
  • An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu
  • Musulmi A Amurka Sun Fara Daukar Matakan Tsaro A Masallatai Saboda Makiya
  • Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko
  • Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu  A Kaduna
  • WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
  • Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa