Aminiya:
2025-11-03@02:06:57 GMT

Ambaliya ta yi ajalin mutane, ta lalata gidaje a Adamawa

Published: 27th, July 2025 GMT

Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutane da dama tare da lalata gidaje a Ƙananan Hukumomin Yola ta Arewa da ta Yola Kudu a Jihar Adamawa.

Ruwan sama mai ƙarfi da ya fara sauka tun da safiyar ranar Lahadi, ya haifar da ambaliya mai tsanani a sassan birnin.

An gabatar da kundin dokar hana cin zarafin mata a Gombe Rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara 650 a Katsina — MSF

Yankunan da lamarin ya shafa sun haɗa da Yola Bye Pass, Sabon Pegi, Yolde Pate, da Modire.

Gidaje da dama sun nutse, gonaki sun lalace, hanyoyi kuma sun katse, lamarin da ya hana mutane da ababen hawa zirga-zirga.

Rahotanni sun nuna cewar mutane da dama sun rasu, ciki har da ƙananan yara.

Ya zuwa yanzu ba san adadin waɗanda suka rasu domin hukumomi na ci gaba da aikin ceto.

“Mutane da yawa sun rasu, musamman yara. Har yanzu muna kan aikin neman mutane. Ba mu taɓa tunanin hakan zai faru ba,” in ji Furera Adamu, wata mazauniyar Sabon Pegi.

Aminiya ta gano yankunan Shagari Low Cost da Sabon Pegi sun cika da ruwa gaba maƙil, wanda hakan ya tilasta wa mazauna yankin barin gidajensu domin neman mafaka a wasu wurare.

Ruwan bai tsaya baya ba har yanzu, wanda hakan zai sa da wuya a iya zama a ciki gidaje a yankin.

Tuni aka yanke wutar lantarki a wasu wuraren da ambaliyar ta fi shafa.

“Muka rasa komai,” in ji wani mazaunin Yola Bye Pass.

“Ruwan ya shigo ta yadda ba mu samu damar ɗebe kayanmu ba.”

Ruwan ya kuma shafe gonaki masu yawa, wanda ya haifar da tsoron za a iya fuskantar ƙarancin abinci a nan gaba.

Maigidanta da dama sun rabu da juna, sannan akwai hatsarin yaɗuwar cututtuka masu nasaba da ruwa sakamakon rashin tsafta a wuraren da ambaliyar ta shafa.

A lokacin haɗa wannan rahoto, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Adamawa (ADSEMA), ba ta fitar da wata sanarwa ba tukuna.

Sai dai Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Adamawa, CP Dankombo Moris, ya tura ‘yan sanda yankin don taimaka wa mutane da ke cikin hatsari.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakaki rundunar, SP Suleiman Yahaya Nguroje, ya fitar a ranar Lahadi.

“Ina mai tabbatar muku da cewa rundunar ‘yan sandan Jihar Adamawa tare da haɗin gwiwar sojoji da ke Yola sun tura jami’ai zuwa wuraren da abin ya shafa domin taimaka wa al’umma,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa an gano gawarwakin mutum biyu zuwa yanzu, kuma an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Modibbo Adama.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamawa Ambaliyar ruwa Jihar Adamawa

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda

A cewar ta a cikin shekarar 2024 jihar Katsina kawai ta samu masu wannan cuta mutum 17 tare da guda biyu a karamar hukumar Danmusa a cikin wannan shekara

Haka kuma Hajiya Zulaihat Radda ya bada tabbacin cewa kowane yaro an tabbatar da ya amshi allurar Riga-kafin shan Inna

Ana jawabin wakilin asusun tallafawa yara na UNICEF na ofishin Kano, Rahama Mohammed Farah ta yabawa kokarin jihar Katsina na dawo da sabon yunkurin kawar cutar shan Inna a Nijeriya baki daya

Ya kuma bayyana cewa asusun kula da kananan yara na UNICEF Yana hadin gwiwa da gwamnatoci da hukumomi da masu ruwa da tsaki a kananan hukumomi domin ganin wajen fadakar da al’umma akan allurar Riga-kafin shan Inna a jihar Katsina.

Shima da yake jawabi shugaban hukumar lafiya a matakin farko ta Jihar Katsina Dakta Shansudeen Yahaya ya yi alkawarin cigaba da wayar da kan al’umma akan wannan cuta ta shan Inna da sauran cututtuka masu kashe yara a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina

Wadanda suka shaida wannan bikin ranar ‘Polio’ ta duniya sun hada da hukumar lafiya ta WHO da kuma masu lalurar cutar shan Inna da wakilan asusun UNICEF da matan shugabannin kananan hukumomi 34 na jihar Katsina

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi October 31, 2025 Manyan Labarai Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai October 31, 2025 Manyan Labarai Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda