Ambaliya ta yi ajalin mutane, ta lalata gidaje a Adamawa
Published: 27th, July 2025 GMT
Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutane da dama tare da lalata gidaje a Ƙananan Hukumomin Yola ta Arewa da ta Yola Kudu a Jihar Adamawa.
Ruwan sama mai ƙarfi da ya fara sauka tun da safiyar ranar Lahadi, ya haifar da ambaliya mai tsanani a sassan birnin.
An gabatar da kundin dokar hana cin zarafin mata a Gombe Rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara 650 a Katsina — MSFYankunan da lamarin ya shafa sun haɗa da Yola Bye Pass, Sabon Pegi, Yolde Pate, da Modire.
Gidaje da dama sun nutse, gonaki sun lalace, hanyoyi kuma sun katse, lamarin da ya hana mutane da ababen hawa zirga-zirga.
Rahotanni sun nuna cewar mutane da dama sun rasu, ciki har da ƙananan yara.
Ya zuwa yanzu ba san adadin waɗanda suka rasu domin hukumomi na ci gaba da aikin ceto.
“Mutane da yawa sun rasu, musamman yara. Har yanzu muna kan aikin neman mutane. Ba mu taɓa tunanin hakan zai faru ba,” in ji Furera Adamu, wata mazauniyar Sabon Pegi.
Aminiya ta gano yankunan Shagari Low Cost da Sabon Pegi sun cika da ruwa gaba maƙil, wanda hakan ya tilasta wa mazauna yankin barin gidajensu domin neman mafaka a wasu wurare.
Ruwan bai tsaya baya ba har yanzu, wanda hakan zai sa da wuya a iya zama a ciki gidaje a yankin.
Tuni aka yanke wutar lantarki a wasu wuraren da ambaliyar ta fi shafa.
“Muka rasa komai,” in ji wani mazaunin Yola Bye Pass.
“Ruwan ya shigo ta yadda ba mu samu damar ɗebe kayanmu ba.”
Ruwan ya kuma shafe gonaki masu yawa, wanda ya haifar da tsoron za a iya fuskantar ƙarancin abinci a nan gaba.
Maigidanta da dama sun rabu da juna, sannan akwai hatsarin yaɗuwar cututtuka masu nasaba da ruwa sakamakon rashin tsafta a wuraren da ambaliyar ta shafa.
A lokacin haɗa wannan rahoto, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Adamawa (ADSEMA), ba ta fitar da wata sanarwa ba tukuna.
Sai dai Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Adamawa, CP Dankombo Moris, ya tura ‘yan sanda yankin don taimaka wa mutane da ke cikin hatsari.
Wannan na cikin wata sanarwa da kakaki rundunar, SP Suleiman Yahaya Nguroje, ya fitar a ranar Lahadi.
“Ina mai tabbatar muku da cewa rundunar ‘yan sandan Jihar Adamawa tare da haɗin gwiwar sojoji da ke Yola sun tura jami’ai zuwa wuraren da abin ya shafa domin taimaka wa al’umma,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa an gano gawarwakin mutum biyu zuwa yanzu, kuma an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Modibbo Adama.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adamawa Ambaliyar ruwa Jihar Adamawa
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da janye dokar ta-baci a Jihar Rivers daga ƙarfe 12 na daren 17 ga watan Satumban 2025.
Shugaban Ƙasar, a wata sanarwa da ya sanya wa hannu, ya ce dokar ta-bacin da ta dakatar da Gwamna, Mataimakiyarsa, da ‘yan majalisar dokokin jihar na tsawon watanni shida ta cimma manufarta na dawo da zaman lafiya a jihar.
Tinubu ya bayyana cewa ya yi amfani da Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin 1999 ne a watan Maris na 2025 sakamakon durƙushewar mulki a Jihar Rivers.
A cewarsa, rashin jituwa tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da Majalisar Dokokin Jihar, da kuma lalata muhimman kadarorin gwamnati sun jefa jihar cikin rikici.
“Lamarin ya kai ga Babbar Kotun Ƙoli ta bayyana a ɗaya daga cikin hukuncinta cewa babu gwamnati a Jihar Rivers.” In ji Shugaban Ƙasa.
Ya gode wa Majalisar Ƙasa bisa amincewa da wannan sanarwa, tare da yabawa Sarakuna da jama’ar jihar bisa haɗin kan da suka bayar.
Tinubu ya kuma yaba wa masu adawa da suka kalubalanci wannan mataki a kotu, yana cewa wannan shi ma wani ɓangare ne na dimokuraɗiyya.
Da yake magana kan sabuwar fahimta tsakanin manyan ‘yan siyasa a jihar, Shugaban Ƙasa ya ce babu dalilin ƙara tsawaita dokar ta-bacin.
Ya bayyana cewa Gwamna Siminalayi Fubara, da Mataimakiyarsa Ngozi Nma Odu, da Shugaban Majalisar Dokoki Martins Amaewhule da dukkan mambobin majalisar jihar za su koma bakin aiki daga 18 ga Satumban 2025.
Tinubu ya yi kira ga shugabannin siyasa a faɗin Najeriya da su ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai domin isar da fa’idodin dimokuraɗiyya ga al’umma.
Daga Bello Wakili