HausaTv:
2025-09-17@22:08:09 GMT

Faransa Zata Bayyana Amincewa Da Samuwar kasar falasdinu

Published: 25th, July 2025 GMT

Shugaban kasar faransa Emanuel macron ya bayyana a jiya Alhamis kan cewa zai shelanta amincewar gwamnatin kasar Faransa da samuwar kasar falasdinu mai cikekken iko a taron babban zauren MDD a cikin watan satumba mai zuwa.

Jaridar ‘Arabnews’ ta kasar saudiya ta nakalto macron yana fadar haka a shafinsa na X ‘ ya kuma kara da cewa, da farko yana son ganin yaki a gaza ya zo karshe, sannan fararen hula da suke gaza su tsira daga kisa da kuma yunwan da aka dora masu.

Kasar faransa dai ita ce babbar kasa a cikin kasashen turai da suka fara amincewa da kasar Falasdinu mai zaman kanta. Kafin haka dai kasashen 140 a duniya sun amince da samuwar kasar falasdinu mai zaman kanta.

A jiya Alhamis gwamnatin kasar faransa a hukumance ta mikawa mataimakin shugaban PLO a birnin Qudus Hussain Al-sheikh. Shugaba Mahmood Abbas yay aba da matsayin da shugaban kasar faransa ya dauka ya kuma gode masa da wannan kokarin.

Kamar yadda aka saba, HKI ta yi allawadai da matsayin na shugaba macron. Haka ma Marco Rubio

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar faransa

এছাড়াও পড়ুন:

Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara

Ɗan takarar jam’iyyar Labour a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Peter Obi, ya ziyarci tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, da kuma sabon Olubadan na Ibadan, Rashidi Ladoja, a wani zagayen ganawa da manyan ’yan siyasa gabanin zaɓen 2027.

Obi, wanda ke ƙoƙarin ƙara yauƙaƙa zumunci da manyan shugabanni a fadin ƙasar, ya bayyana cewa ziyarar na da alaƙa da burinsa na ganin an samu shugabanci na gaskiya da riƙon amana a Najeriya.

An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya bayyana cewa ziyararsa ta musamman zuwa Ibadan na da nufin girmama Rashidi Ladoja, wanda aka naɗa a matsayin Olubadan, da kuma jaddada muhimmancin Ibadan a siyasa, zamantakewa, da tattalin arzikin ƙasar.

“Na kai ziyara don girmama sabon Olubadan, Rashidi Ladoja, wanda ƙwarewarsa a matsayin tsohon sanata, gwamna, kuma attajiri za ta taimaka wajen ɗaga martabar Ibadan,” in ji Obi.

Ya ƙara da cewa tattaunawarsa da Obasanjo da Ladoja na da nasaba da ci gaban Najeriya da kuma shugabanci da ke da burin sauya al’umma ta fuskar gaskiya da adalci.

Ziyarar Obi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, inda ake hasashen zai sake tsayawa takarar shugaban ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
  • Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar