Wakilin dindindin na kasar Sin a Majalisar Dinkin Duniya, Fu Cong, ya yi magana a wani taro na bude kofar Kwamitin Sulhu na MDD game da hadin gwiwa tsakanin MDD da kungiyar hadin gwiwar kasashen Musulmi (OIC), inda ya karyata batun da wakiliyar Amurka ta yi game da yankin Xinjiang na Sin.

Fu Cong ya ce, Sin ta nuna adawa kwarai tare da kin amincewa da zargi mara tushe balle makama da wakiliyar Amurka ta yi game da Xinjiang.

A halin yanzu jihar Xinjiang na cikin kwanciyar hankali, tana samun ci gaban tattalin arziki, al’umma suna rayuwa cikin kwanciyar hankali, kuma suna cikin mafi kyawun yanayin ci gaba a tarihi. Amma da gangan Amurka ke kokarin yayata batun Xinjiang da nufin tsoma baki cikin harkokin cikin gida na Sin da kuma hana ci gaban Sin, wanda karara ya bayyana gaskiyar nuna son rai kawai, da kuma kasancewa mai fuska biyu.

Fu Cong ya kuma bayyana cewa, a cikin shekaru shida da suka gabata, sama da kasashe 100, ciki har da kasashe masu bin addinin Musulunci da dama, sun nuna goyon bayansu ga madafun iko na Sin a kwamiti na uku na babban taron MDD da nuna adawa da siyasantar da batun kare hakkin dan Adam da kuma amfani da shi a matsayin hanyar tsoma baki cikin harkokin cikin gida na wasu kasashe. Wannan ya tona asirin makircin Amurka na “amfani da Xinjiang don hana ci gaban Sin”, kuma mugun nufinta na tayar da husuma a tsakanin kasashe ya ci tura. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Miyagun Kwayoyi A Kano

Mambobin kwamitin sun haɗa da:

1. Barr. Aminu Hussain – Shugaba

2. Barr. Hamza Haladu – Mamba

3. Barr. Hamza Nuhu Dantani – Mamba

4. Alhaji Abdullahi Mahmoud Umar – Mamba

5. Manjo Janar Sani Muhammad (Rtd.) – Mamba

6. 6. Kwamared Kabiru Said Dakata – Mamba

7. Hajiya Bilkisu Maimota – Sakatariya

Yayin da yake sanar da kafa kwamitin, Gwamna Yusuf ya nuna matuƙar damuwarsa game da zargin da ke kan jami’in gwamnati, tare da jaddada aniyarsa ta yaƙi da safarar miyagun ƙwayoyi da duk wasu munanan ɗabi’un da ba su dace ba a fadin jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano
  • Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Miyagun Kwayoyi A Kano
  • Miliyoyin Al’ummar Yemen Sun Fito Taron Gangamin Nuna Goyon Baya Ga Falasdinawa
  • Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 
  • Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda
  • Iran: Iran Tana Cikin Kasashe Biyar Na Duniya Da Suka Ci Gaba Wajen Kiwon Dabbobi
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Fara Tattaunawa kan Masifar Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya