Manoma A Kirikasamma Sun Yaba Wa Gwamna Namadi Bisa Rangwaman Takin Zamani
Published: 27th, July 2025 GMT
Duba da tsadar kayayyakin noma da ke kara ta’azzara a fadin kasar nan, da kuma janye hannun manoma da dama daga noman shinkafa da masara sakamakon tsadar taki,Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya kaddamar da rangwamin kashi 45 zuwa 50 cikin 100 na farashin buhun taki, tare da tura manyan motocin daukar kaya domin rarraba takin a kananan hukumomi 27 na jihar.
Rediyon Nigeria ya ruwaito cewa, karamar hukumar Kirikasamma ta karbi buhuna 1,200 da za a sayar wa manoma a farashi mai rangwame.
Shugaban sashen aikin gona da albarkatun kasa na karamar hukumar, Alhaji Sabi’u Kani, ya bayyana cewa za a sayar da buhun takin NPK na kamfanin Solar Brand a kan 28,800.
Yayin kaddamar da fara sayar da takin a gundumomi 10 na Kirikasamma, Shugaban karamar hukumar, Alhaji Muhammad Maji Wakili Marma, ya ce wannan mataki na Gwamna Namadi na nufin rage wa manoma radadin tsadar taki a kasuwanni.
Marma ya kara da cewa, “Kwamitocin gundumomi karkashin jagorancin kansiloli za su jagoranci rabon takin, tare da sauran mambobi na kowace gunduma.”
Shi ma da yake jawabi, Shugaban Kungiyar Manoman Najeriya (AFAN) reshen Kirikasamma, Kabila Suga, ya jinjinawa shugaban karamar hukumar da Gwamna Umar Namadi bisa wannan rangwame da zai taimaka wa manoma.
Kabila ya kara da cewa farashin buhu daya ta NPK a kasuwa ya kai kimanin Naira 50,000 zuwa 56,000, wanda ya fi karfin yawancin kananan manoma.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa karamar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Saboda wannan baiwa daga Allah, iyalai da ‘yan uwan mai akuyar suka sanar da shirye-shiryen gudanar da bikin murnar haihuwar ‘ya’yan akuyar a ranar Lahadi mai zuwa a Garun Dakasoye, karamar hukumar Garun Malam ta Jihar Kano, inda za a yi musu suna da kuma karatun Alkur’ani mai girma.
A nasa bangaren, mahaifin budurwar, Malam Aliyu dake Garin Dakasoye, ya tabbatar da cewa za su gudanar da bikin domin nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki bisa wannan ni’ima da ya ba su.
Ya kara da cewa: “Mun gode wa Allah bisa wannan arziki, kuma muna sa ran gudanar da bikin tare da sanya musu suna domin nuna godiya ga Allah mai daukaka.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp