Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Karyata Rade-radin Sayarda Makarantar Yusuf Dan-tsoho
Published: 24th, July 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kaduna ta karyata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke cewa ana shirin sayar da makarantar firamare ta Yusuf Dantsoho da ke Unguwar Rimi GRA.
Kwamishinan Harkokin Kananan Hukumomi da Masarautu, Alhaji Maman Lagos, ne ya bayyana hakan a lokacin da ya kai ziyarar aiki makarantar.
Makarantar Yusuf Dantsoho, wacce aka kafa a shekarar 1920, tana tsakiyar Unguwar Rimi GRA, kuma ta samar da fitattun ‘yan Najeriya da dama da suka yi aiki a matakai daban-daban na gwamnati da kuma masu zaman kansu.
Alhaji Maman Lagos ya tabbatar da cewa Gwamnatin Jihar Kaduna ba ta da niyyar sayar da wata cibiyar gwamnati, kama daga makarantu zuwa asibitoci.
Yace maimakon haka, gwamnati na da kudurin inganta da fadada irin wadannan cibiyoyin domin su fi amfani wa al’umma.
Alhaji Maman Lagos ya kalubalanci duk wanda ke da ikirarin ya sayi makarantar da ya fito da takardun shaida.
Ya ce gwamnatin Malam Uba Sani ba za ta sayar da makarantu mallakin gwamnati ba.
Haka kuma, ya bukaci iyaye da mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu su kuma yi watsi da jita-jita marasa tushe.
A nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Kaduna ta Arewa, Muhammad Gambo, ya tabbatar da cewa makarantar Yusuf Dantsoho tana karkashin kulawar hukumar kananan hukumomi kamar yadda aka saba.
Wani jigo a harkokin makarantar, Abubakar Kantoma, ya bayyana cewa wasu ‘yan gine-gine sun yi yunkurin fara aiki a cikin harabar makarantar, amma aka dakatar da su saboda rashin bayyananniyar hujja.
Radio Nigeria ta kuma tattauna da wasu daliban makarantar wadanda suka nuna damuwa kan jita-jitar da ake yadawa.
Makarantar dai ta rufe ne a lokacin ziyarar saboda hutun karshen zangon karatu.
COV: Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamnatin Jihar Karyata Makarantar Rade radin Sayarda
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.