Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: Taro Tsakanin Iran Da Tawagar Kasashen Turai Dama Ce Ta Gyarar Tunanin Tarai
Published: 25th, July 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Taron Istanbul wata dama ce ta gyara matsayar Turai kan shirin makamashin nukiliyar Iran
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i, ya yi la’akari da taron na yau tsakanin Iran da kasashe uku mambobin kungiyar hadin gwiwa ta JCPOA a matsayin wata muhimmiyar dama ta gyara ra’ayoyinsu da gwada hakikaninsu kan batun makamashin nukiliyar kasar Iran.
A cikin wata sanarwa da ya aikewa kamfanin dillancin labaran IRNA, Isma’il Baqa’i ya bayyana fatansa na cewa wadannan kasashe uku za su yi amfani da wannan damar wajen gyara tsarin da suka bi a baya wanda bai dace ba, wanda ya lalata martabar Turai da matsayin tattaunawa, tare da mayar da ita a matsayin yar wasa maras tushe.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ya bayyana takaicinsa game da matsayin kasashen Turai uku na nuna son zuciya dangane da wuce gona da iri da gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka suka dauka kan kasar Iran – wadanda suka gabatar da wadannan kasashe uku ga duniya a matsayin tushe haifar da hargitsi da mara wa ta’addanci gindi. Ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran a baya ta yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da irin wadannan matsayar da ba ta dace ba, kuma tabbas a taron na yau Juma’a za a isar da zanga-zangar Iran dangane da hakan ga bangarorin Turai, kuma za a bukaci su yi karin haske.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ayatullahi Makarem Shirazi Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Hadin kai Da Suka Bayar Lokacin Yakin Kwanaki 12
Ayatullah Makarem Shirazi ya jaddada cewa: An kara samun karfafan hadin kan al’umma Iran bayan wuce gona da irin ‘yan sahayoniyya da Amurka kan kasarsu
Ayatullah Nasser Makarem Shirazi, babban malamin addinin Musulunci a birnin Qum mai tsarki na kasar Iran ya jaddada cewa: An kara samun hadin kan kasa bayan yakin wuce gona da iri da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka kaddamar kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
A yayin ganawarsa da shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian a jiya Laraba a birnin Qom mai alfarma Ayatullah Makarem Shirazi ya yi ishara da yakin tunani da gwamnatin ‘yan Sahayoniyya da Amurka suka yi kan Iran yana mai cewa: Wadannan makiya sun yi zaton za su haifar da rudani ta hanyar kai wa Iran hari, amma alhamdulillahi ba wai kawai hakan ya faru ba, amma hadin kan al’ummar kasar ya kara karfafa. A wani bangare na jawabin nasa, Ayatullah Makarem Shirazi ya bayyana wasu manyan matsaloli guda uku da al’umma ke fuskanta: hauhawar farashin kayayyaki, gidajen haya, da samar da ayyukan yi ga matasa. Ya ce, “Dole ne a yi kokarin magance wadannan matsalolin, kuma in Allah idan ya yarda za a yi nasara.”