Burtaniya Zata Fara Jefawa Falasdinawa Abinci Daga Sama
Published: 26th, July 2025 GMT
Firai ministan kasar Burtaniya Keir Starmer ya bayyana cewa ya fara tuntubar wasu kasashen turai kan nshirin jefawa Falasdinawa abinci daga sama tare da taimakon kasar Jordan.
Shafin yanar gizo na Arab News ya nakalto Starmer yana fadar haka a yau Asanar ya kuma kara da cewa ya yi magana da kasashen Faransa da Jamus kan wannan shirin.
Labarin ya kara da cewa banda jefa masu abinci kasashen zasu sauka su dauki marasa lafiya musamman yara kanana don jinyarsu..
Tun kimani watanni 4 da suka gabata ne gwamnatin HKI ta rufe kofofin shiga zirin gaza ta kuma hana shigowar abinci da magunguna, da nufin kashe dukkan falasdinawa kimani miliyon biyu a Gza, don ginawa yahudawa matsugunai a yankin.
Tun fara yakinn tufanul aksa a ranar 07 ga watan Octoban shekara 2023 ya zuwa yanzu sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa fiye da dubu 60 a yayinda wasu fiye da dubu 150 suka ji rauni.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mata da yara a sabon harin Filato
Aƙalla mutum 14; ciki har da mata da ƙananan yara ƙanana ne, suka rasu a wani sabon hari da aka kai a Jihar Filato.
Harin ya faru ne da yammacin ranar Alhamis a Gundumar Mangor da ke Ƙaramar Hukumar Bokkos.
Sarkin Katsinan Gusau ya rasu Yadda aka mayar da yaran da aka sace a Kano masu wanke-wanke a KuduWaɗanda aka kashe suna kan hanyarsu ta dawowa daga kasuwar mako-mako da ke garin Bokkos, lokacin da wasu ’yan bindiga suka buɗe musu wuta.
Wannan hari na zuwa ne wata guda bayan wani hari da aka kai wa wasu ‘yan ɗaurin aure daga Zariya a Jihar Filato, inda aka kashe su.
Ƙungiyar Bokkos Cultural Development Forum (BCDF), ta tabbatar da faruwar harin.
Shugaban ƙungiyar, Farmasum Fuddang, ya ce suna jimami da ɓacin rai saboda wannan hari, musamman ganin cewa an sha gudanar da zaman sulhu tsakanin manoma da makiyaya.
Ya ƙara da cewa mata da ƙananan yara na daga cikin waɗanda suka rasu.
Fuddang, ya danganta harin da wata ƙabila.
Ya kuma ce wata ƙungiyar ta’addanci tana ƙone ƙauyuka da ƙwace gonaki a yankin Mushere.
A cewarsa, burinsu shi ne su mamaye dukkanin Ƙaramar Hukumar Bokkos, wadda ta ke hedikwatar noman dankalin turawa a Najeriya.
Sai dai makiyaya a yankin sun ce ba su da hannu a cikin harin.
Shugaban Gan Allah Fulani Development Association (GAFDAN) na yankin, Saleh Adamu, ya karyata zargin, inda ya bayyana cewa babu wata shaida da ke nuna cewa Fulani ne suka kai harin.
Ya ce ba a kama ko mutum ɗaya daga cikin makiyaya a wajen da harin ya auku ba, kuma ya ce wannan zargi sabon abu ne da bai taɓa faruwa a yankin ba.
Saleh ya ƙara da cewa, “A duk lokacin da wani abu ya faru, jami’an tsaro su kan gudanar da bincike kafin a gano waɗanda suka aikata laifin. Muna Allah-wadai da wannan hari baki ɗaya.
“Kisan mutane marasa laifi ba shi da wani uzuri da za a aminta da shi.”
A halin yanzu, jami’an tsaro ba su fitar da wata sanarwa dangane da harin ba.
Wakilinmu ya tuntuɓi jami’an hulɗa da jama’a na Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, da na rundunar ’yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred, amma ba su ce komai ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.