Tsibirin Ciniki Maras Shinge Na Hainan Na Ci Gaba Da Jawo Hankalin Jarin Waje
Published: 24th, July 2025 GMT
Aikin gina tsibirin ciniki maras shinge na Hainan na kasar Sin ya samu gagarumin ci gaba sosai, inda gwamnatin kasar Sin ta sanar a jiya cewa, a ranar 18 ga watan Disamban bana, za a kaddamar da manufar kafa “kwastam mai zaman kansa a duk faɗin tsibirin ciniki maras shinge na Hainan” a hukumance, wadda ke nufin saukaka bincike da ragewa ko soke haraji.
Ga kasar Sin, gina tsibirin ciniki maras shinge na Hainan wata babbar manufa ce ta kasa, wadda ke nuna matsayin koli na bude kofa ga kasashen duniya.
Bayan aiwatar da manufar, duk tsibirin Hainan zai zama yanki na musamman a karkashin kulawar hukumar kwastam, za a aiwatar da manufofi mafi ’yanci kuma masu sauki, da za su shafi fannoni guda hudu, wato, manufar soke harajin kayayyaki, matakan saukaka harkokin kasuwanci, matakan zirga-zirga masu dacewa da kuma tsarin sa ido mai inganci.
Dauki manufar “soke haraji” a matsayin misali. Bayan manufar ta fara aiki a duk fadin tsibirin Hainan, za a fadada adadin kayayyakin da ba su da haraji daga 1,900 a yanzu zuwa kusan 6,600, wanda ya kai kusan kashi 74 bisa dari na dukkan rukunonin harajin kayayyaki, kuma ya karu da kashi 53 bisa dari idan aka kwatnta da yawan kayayyakin da ake shigowa kafin a aiwatar da manufar. Wannan zai rage dimbin kudaden da ake kashewa wajen shigowa da kayayyaki, da kara kuzarin yin kasuwanci, da kuma samar da riba ga masu sayayya da ’yan kasuwa. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.