Aikin gina tsibirin ciniki maras shinge na Hainan na kasar Sin ya samu gagarumin ci gaba sosai, inda gwamnatin kasar Sin ta sanar a jiya cewa, a ranar 18 ga watan Disamban bana, za a kaddamar da manufar kafa “kwastam mai zaman kansa a duk faɗin tsibirin ciniki maras shinge na Hainan” a hukumance, wadda ke nufin saukaka bincike da ragewa ko soke haraji.

“Ana iya cin moriyar manufofin ba da fifikon harajin kudi a tsibirin Hainan”, sannan “mu’amalar Hainan da kasashen duniya za ta kasance cikin ’yanci da lumana”. A ra’ayin jama’a na kasa da kasa, wannan wani muhimmin mataki ne ga kasar Sin na kara fadada bude kofa ga ketare, wanda ba bunkasa ci gaban tattalin arzikin kasar kadai zai yi ba, har da samar da damammaki ga duniya.

Ga kasar Sin, gina tsibirin ciniki maras shinge na Hainan wata babbar manufa ce ta kasa, wadda ke nuna matsayin koli na bude kofa ga kasashen duniya.

Bayan aiwatar da manufar, duk tsibirin Hainan zai zama yanki na musamman a karkashin kulawar hukumar kwastam, za a aiwatar da manufofi mafi ’yanci kuma masu sauki, da za su shafi fannoni guda hudu, wato, manufar soke harajin kayayyaki, matakan saukaka harkokin kasuwanci, matakan zirga-zirga masu dacewa da kuma tsarin sa ido mai inganci.

Dauki manufar “soke haraji” a matsayin misali. Bayan manufar ta fara aiki a duk fadin tsibirin Hainan, za a fadada adadin kayayyakin da ba su da haraji daga 1,900 a yanzu zuwa kusan 6,600, wanda ya kai kusan kashi 74 bisa dari na dukkan rukunonin harajin kayayyaki, kuma ya karu da kashi 53 bisa dari idan aka kwatnta da yawan kayayyakin da ake shigowa kafin a aiwatar da manufar. Wannan zai rage dimbin kudaden da ake kashewa wajen shigowa da kayayyaki, da kara kuzarin yin kasuwanci, da kuma samar da riba ga masu sayayya da ’yan kasuwa. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Ficewar Amurka daga yarjejeniyoyin kasa da kasa da hukumomin duniya ba sabon labari ba ne, don haka mene ne abun mamaki idan ta bar UNESCO a karo na uku? Wani binciken jin ra’ayoyin jama’a da CGTN ta gudanar ya nuna cewa kashi 84.2 cikin dari na wadanda suka bayyana rayoyinsu ba su yi mamakin wannan matakin ba, lamarin da ke nuni da cewa, kasashen duniya sun saba da halayyar “kauracewar” Amurka. Wannan mataki na “Amurka ta zamanto farko” yana kara ingiza bukatar tsarin damawa da mabambantan bangarori na hakika cikin hanzari.

Hujjar gwamnatin Amurka a wannan karon ta kasance a sarari, watau ta zargi UNESCO da ci gaba da zurfafa tabbatar da “mabambantan tsarin zamantakewa da al’adu” wadanda suka ci karo da manufarta ta “Amurka ta zamanto farko”. A cewar sakamakon binciken, kashi 93.5 na masu bayyana raayoyi sun soki Amurka bisa mayar da cibiyoyin kasa da kasa a matsayin kayan aikin cimma muradunta na siyasa.

Binciken jin ra’ayoyin ya nuna cewa kashi 90.7 cikin dari na wadanda suka bayyana raayoyinsu suna kallon ficewar baya-bayan nan a matsayin karin tabbaci na yadda Amurka ke nuna son zuciya saboda Isra’ila, yayin da kashi 91.1 cikin dari na jamaar da suka bayyana raayoyin nasu suka nuna cewa, tsarin mu’amalarta da hukumomin kasa da kasa bai zamo mai alfanu ga wata babbar kasa ba, ko kuma biyan bukatun kasashen duniya.

Wanda aka gudanar a kafofin CGTN na harsunan Ingilishi, da Sifaniyanci, Faransanci, Larabci, da Rashanci, binciken ya tattaro raayoyin jamaa 9,097 cikin sa’o’i 24. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
  • Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje
  • Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jaddada Aniyar Iran Ta Ci Gaba Da Inganta Sinadarin Uranium
  • Iran: Iran Tana Cikin Kasashe Biyar Na Duniya Da Suka Ci Gaba Wajen Kiwon Dabbobi
  • Asusun Kula Da Kananan Yara Na Majalisar Dinkin Duniya “UNICEF” Ya Yi Gargadi Kan Bala’in Jin Kai A Gaza
  • Gwamantin Kasar Siriya Ta Rufe Hanyoyin Shiga BirninSiweida Na Kasar Saboda Ci Gaba Da Bullar Rikici
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza