HausaTv:
2025-07-27@04:14:45 GMT

DR Congo: M23 Ta Yi Barazanar Kauracewa Sulhu da Gwamnatin Kongo

Published: 26th, July 2025 GMT

Kungiyar yan tawaye M23 wacce take iko da yanki mai yawa a gabacin Democradiyyar Kongo ta bada sanarwan cewa idan gwamnatinn kasar Kongo bada gaggauta sakin fursinonin kungiyar ba, to tana iya kauracewa tattaunawan da za’a gudanar a birnin Doha na kasar Qatar a watan mai zuwa.

Shafin yanar gizo na Africanews ya nakalto babban sakataren kungiyar kuma mai magana da yawunta yana fadar haka a ranar jumma’a.

Ya kuma kara da cewa bayan da kowa ya bayyana matsayinsa a wata mai zuwa ne ake saran bangarorin biyu wato gwamnatin kongo da kuma kungiyar M23 zasu rattaba hannu a kan yarjeniyar sulhu na gaskiya.

Ya ce tattaunawa da kuma amincewa da wasu ka’idoji wanda bangarorin biyu suka rattabawa hannu a watan da ya wuce a doha, sharer fage ne na yarjeniyar da za’a rattabawa hannu a ranar 18 ga watan Augusta mai zuwa a birnin Doha na kasar Qatar.  Benjamin Mbonimpa ya jaddada cewa a cikin alkawalin da suka dauka a taron Doha na farko shi ne a saki fursinonin M23 kafin taro nag aba, don haka idan an ki yin haka tabbas ba zamu je taro na gabata.

A halinn yanzu dai kungiyar M23 suna iko da mafi yawan lardin kivu na gabacin kasar Kongo.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Brazil Ta Shiga Yaki Da HKI, Inda Ta Kudurin Anniyar Goyon bayan Afirka Ta Kudu A Kotun ICJ

Gwamnatin kasar Brazil tana shirin bayyana goyon bayanta ga Afirka ta kudu a karar da ta shigar a gaban kotun ICJ dangane da tuhumar jami’an gwamnatin HKI da aikaya kisan kiyashi a Gaza.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wata jaridar kasar Brazil Folha De S tana fadar haka. Sannan kamfanin dillancin labaran reuters ya tabbatar da labarin a jiya Laraba.

A shekara ta 2023 ne gwamnatin Afirka ta kudu ta shigar da karar don tabbatar da cewa gwamnatin HKI ta na aikata kissan kare dangi kan kasar Amurka. Wanda ya sabawa dokar hana kissan kare dangi ta MDD ta shekara 1948.

Sannan a cikin watan Octoban da ya gabata ne, Pretoria ta gabatar da shaidu da bayanai da suke tabbatar da ikrarinta a gaban alkalan kotun a birnin Hague cibiyar kotun. Wannan ya sa kotun ta fidda sammacin kama firai ministan HKI Benyamin Natanyahu da kuma ministansa na yaki a lokacin Aut galant.

Kasashen duniya da dama sun amince da sammacin, sun kuma dauki alkawalin kama so a duk lokacinda suka kuskura suka shiga kasashensu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
  • Rasha Ta Sha Alwashin Mayar Wa Da Nato Martani Mai Tsanani Idan Ta Kai Ma Ta Hari
  • Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
  • Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
  • ‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8
  • ‘Yan Tawayen Sudan Ta Kungiyar Rapid Support Forces Sun Kashe Mutane 27 A Yammacin Jihar Kordofan Ta Kasar Sudan
  • ‘Yan Nijeriya Miliyan 40 Ke Fuskantar Barazanar Kwararowar Hamada – Ministan Muhalli
  • Kungiyar “Human Right Watch” Ta Yi Kira Da A Saki Tsohon Shugaban Kasar Nijar Muammad Bazoum
  • Brazil Ta Shiga Yaki Da HKI, Inda Ta Kudurin Anniyar Goyon bayan Afirka Ta Kudu A Kotun ICJ