Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin dindindin na kasar Sin a Majalisar Dinkin Duniya, Fu Cong, ya yi magana a wani taro na bude kofar Kwamitin Sulhu na MDD game da hadin gwiwa tsakanin MDD da kungiyar hadin gwiwar kasashen Musulmi (OIC), inda ya karyata batun da wakiliyar Amurka ta yi game da yankin Xinjiang na Sin.

Fu Cong ya ce, Sin ta nuna adawa kwarai tare da kin amincewa da zargi mara tushe balle makama da wakiliyar Amurka ta yi game da Xinjiang. A halin yanzu jihar Xinjiang na cikin kwanciyar hankali, tana samun ci gaban tattalin arziki, al’umma suna rayuwa cikin kwanciyar hankali, kuma suna cikin mafi kyawun yanayin ci gaba a tarihi. Amma da gangan Amurka ke kokarin yayata batun Xinjiang da nufin tsoma baki cikin harkokin cikin gida na Sin da kuma hana ci gaban Sin, wanda karara ya bayyana gaskiyar nuna son rai kawai, da kuma kasancewa mai fuska biyu.

Fu Cong ya kuma bayyana cewa, a cikin shekaru shida da suka gabata, sama da kasashe 100, ciki har da kasashe masu bin addinin Musulunci da dama, sun nuna goyon bayansu ga madafun iko na Sin a kwamiti na uku na babban taron MDD da nuna adawa da siyasantar da batun kare hakkin dan Adam da kuma amfani da shi a matsayin hanyar tsoma baki cikin harkokin cikin gida na wasu kasashe. Wannan ya tona asirin makircin Amurka na “amfani da Xinjiang don hana ci gaban Sin”, kuma mugun nufinta na tayar da husuma a tsakanin kasashe ya ci tura. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD
  • Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 
  • Gwamnatin Bauchi Ta Cire Shugaban Makaranta Kan Satar Kayan Gwamnati
  • An rantsar da Nentawe sabon shugaban APC na ƙasa
  • Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa
  • Yawan Ma’aikata Ne Ya Hana Borno Fara Biyan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi – Zulum
  • Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa
  • DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta