Jiya Juma’a an kammala zagayen karshe na gasar kirkire-kirkire, ta daliban kasa da kasa ta kasar Sin ta yankin Afirka a birnin Nairobin kasar Kenya, wadda jami’ar koyon ilmin aikin gona ta Nanjing ta kasar Sin ta karbi bakuncin shiryawa. Wannan shi ne karon farko da aka gudanar da gasar a nahiyar Afirka.

Rahotanni na cewa, an gudanar da gasar ne a tsawon kwanaki biyu, kuma dalibai 559 daga jami’o’in Afirka 115 sun yi rajitar halartar gasar, kana an baje kayayyakin shiga gasar har 185, wadanda suke shafar fasahohin aikin noma da abinci, da amfani da basirar AI, da kiyaye muhalli, da samun ci gaba mai dorewa da sauransu.

A karshe, alkalan gasar sun tattauna, tare da tsai da kudurin bayar da lambobin yabo ga tawagogi 30 na jami’o’i 21 daga kasashe 9. A cikinsu, tawagar jami’ar Egerton ta kasar Kenya, ta samu lambar yabo ta zinari bisa aikin da ta gabatar na dasa tsiron tumatir a jikin wata bishiya ta daban.

Mataimakiyar shugaban jami’ar koyar da ilmin aikin gona ta Nanjing Zhu Yan, ta bayyana cewa, an gudanar da gasar kirkire-kirkire ta daliban kasa da kasa ta kasar Sin ta yankin Afirka karo na farko ne, don sa kaimi ga matasan Sin da Afirka, da su yaukaka mu’amalar al’adu da juna, da kokarin yin kirkire-kirkire tare, da kuma nazarin samar da ci gaba mai dorewa tare. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Saboda wannan baiwa daga Allah, iyalai da ‘yan uwan mai akuyar suka sanar da shirye-shiryen gudanar da bikin murnar haihuwar ‘ya’yan akuyar a ranar Lahadi mai zuwa a Garun Dakasoye, karamar hukumar Garun Malam ta Jihar Kano, inda za a yi musu suna da kuma karatun Alkur’ani mai girma.

 

A nasa bangaren, mahaifin budurwar, Malam Aliyu dake Garin Dakasoye, ya tabbatar da cewa za su gudanar da bikin domin nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki bisa wannan ni’ima da ya ba su.

 

Ya kara da cewa: “Mun gode wa Allah bisa wannan arziki, kuma muna sa ran gudanar da bikin tare da sanya musu suna domin nuna godiya ga Allah mai daukaka.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Bida Poly ta kawo sojoji su kula da jarrabawar ɗalibai
  • Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya
  • Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar
  • Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin