An Kashe Sojojin HKI 3 A Yankin Khan-Yunus Na Gaza
Published: 27th, July 2025 GMT
Da safiyar Yau Lahadi Adadin sojojin mamaya na HKI da aka kashe a yankin Khan-Yunus sun kai 3.
Jaridar Yediot Ahranot ta ‘yan sahayoniya ta buga labarin cewa; An kuma kashe waji jami’in soja na rundunar Gulani ta hanyar fashewar nakiya da aka dasa akan hanyar motarsa a jiya Asabar a Kudancin Gaza.
Har ila yau jaridar ta ce, an kuma jikkata wani jami’in sojan mamayar bayan da nakiya ta daki wata motar jigilar sojoji.
A nata gefen, rundunar Kassam ta kungiyar Hamas ta sanar da kai wa motar daukar sojojin HKI hari ta hanyar nakiyar da ta dasa a gidan gaban motar.
Bugu da kari dakarun na Kassam sun sanar da kai wani harin akan motar soja ta 3 ta hanyar amfani da makamin “al-Yassin 105” a yankin Abasan al-Kabirah dake Khan Yunus.
Haka nan kuma dakarun na Kassam sun ce, mayakansu sun ga yadda sojojin na mamaya su ka binne motocin da su ka kone, da kuma saukar jiragen sama masu saukar angulu domin daukar gawawwaki da wadanda jikkata.
Duk da cewa sojojin na HKI sun dauki shekaru biyu suna kisan kiyashi a Gaza, sai dai duk da haka bai hana ‘yan gwgawarmaya fitowa suna kashe su da jikkata su ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
Rahotanni sun bayyana cewa, wata gobara ta ƙone wani shagon Adidas Sports da ke cikin rukunin babban kantin nan na sayar da kayayyaki na Jabi Lake Mall, Abuja da tsakar daren Alhamis.
Daily Trust ta ruwaito cewa, shagon ne kaɗai gobarar ta shafa.
An kuma samu rahoton cewa, an baza jami’an kashe gobara daga Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, da na Kamfanin Berger da na hukumar kashe gobara ta Abuja da kuma jami’an ’yan sanda zuwa wurin.
Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29A lokacin da Wakilin Daily Trust ya kai ziyara da safe zuwa wurin, an shawo kan gobarar.
Wani ma’aikaci a shagon ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:00 na tsakar daren ranar Alhamis.
Ya ce, ba a samu asarar rai ba a wurin. Ya kuma tabbatar da cewa, “Shagon sayar da kayan Wasannin Adidas ne kawai gobarar ta shafa.”
Mai magana da yawun Hukumar kashe gobara ta babban birnin tarayya, Ibrahim Mohammad, ya tabbatarwa da majiyar da faruwar lamarin, amma ya ce ƙarama ce.
Ya ce, an shawo kan lamarin kuma an dawo da zaman lafiya.
Ita ma da take mayar da martani, kakakin rundunar ’yan sandan Birnin Tarayya, Josephine Adeh ta ce an tura jami’an ’yan sanda wurin da lamarin ya faru domin kare yankin da kuma hana sace-sacen jama’a.
“Mun samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 3:40 na asubahi, nan take muka tura mutanenmu wurin domin su tsare wurin da kuma hana duk wani abu da ya saɓa wa zaman lafiya,” in ji ta.