Aminiya:
2025-11-02@19:55:57 GMT

An kashe mata da yara a sabon harin Filato

Published: 25th, July 2025 GMT

Aƙalla mutum 14; ciki har da mata da ƙananan yara ƙanana ne, suka rasu a wani sabon hari da aka kai a Jihar Filato.

Harin ya faru ne da yammacin ranar Alhamis a Gundumar Mangor da ke Ƙaramar Hukumar Bokkos.

‎Sarkin Katsinan Gusau ya rasu Yadda aka mayar da yaran da aka sace a Kano masu wanke-wanke a Kudu

Waɗanda aka kashe suna kan hanyarsu ta dawowa daga kasuwar mako-mako da ke garin Bokkos, lokacin da wasu ’yan bindiga suka buɗe musu wuta.

Wannan hari na zuwa ne wata guda bayan wani hari da aka kai wa wasu ‘yan ɗaurin aure daga Zariya a Jihar Filato, inda aka kashe su.

Ƙungiyar Bokkos Cultural Development Forum (BCDF), ta tabbatar da faruwar harin.

Shugaban ƙungiyar, Farmasum Fuddang, ya ce suna jimami da ɓacin rai saboda wannan hari, musamman ganin cewa an sha gudanar da zaman sulhu tsakanin manoma da makiyaya.

Ya ƙara da cewa mata da ƙananan yara na daga cikin waɗanda suka rasu.

Fuddang, ya danganta harin da wata ƙabila.

Ya kuma ce wata ƙungiyar ta’addanci tana ƙone ƙauyuka da ƙwace gonaki a yankin Mushere.

A cewarsa, burinsu shi ne su mamaye dukkanin Ƙaramar Hukumar Bokkos, wadda ta ke hedikwatar noman dankalin turawa a Najeriya.

Sai dai makiyaya a yankin sun ce ba su da hannu a cikin harin.

Shugaban Gan Allah Fulani Development Association (GAFDAN) na yankin, Saleh Adamu, ya karyata zargin, inda ya bayyana cewa babu wata shaida da ke nuna cewa Fulani ne suka kai harin.

Ya ce ba a kama ko mutum ɗaya daga cikin makiyaya a wajen da harin ya auku ba, kuma ya ce wannan zargi sabon abu ne da bai taɓa faruwa a yankin ba.

Saleh ya ƙara da cewa, “A duk lokacin da wani abu ya faru, jami’an tsaro su kan gudanar da bincike kafin a gano waɗanda suka aikata laifin. Muna Allah-wadai da wannan hari baki ɗaya.

“Kisan mutane marasa laifi ba shi da wani uzuri da za a aminta da shi.”

A halin yanzu, jami’an tsaro ba su fitar da wata sanarwa dangane da harin ba.

Wakilinmu ya tuntuɓi jami’an hulɗa da jama’a na Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, da na rundunar ’yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred, amma ba su ce komai ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hari Makiyaya yara

এছাড়াও পড়ুন:

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shi ma wasan da ta yi nasara a kan kungiyar Sifaniya a daf da za a tashi ta ci kwallon a gasar Zakarun Turai da na Newcastle United a Premier League. Tun daga nan alamomi suka fara bayyana cewar akwai tarin matsaloli a Liberpool, wadda kowanne wasa kwallo ke shiga ragarta in ban da wanda ta yi nasara a kan Arsenal 1-0 a Premier League cikin Agusta da wanda ta ci Burnley 1-0 a cikin watan Satumba a Premier League.

Sababbnin ‘Yanwasan da Liberpool ta saya a kakar banamages Giorgi Mamardashbili daga Balencia Jeremie Frimpong daga Bayern Leberkusen, Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen,

Milos Kerkez daga Bournemouth, Hugo Ekitike daga Eintracht Frankfurt, Aledander Isak daga Newcastle United, Armin Pecsi daga Puskas Akademia. Giobanni Leoni daga Parma Freddie Woodman daga Preston North, Will Wright daga Salford.

Wasu daga cikin matsalolin Liberpool A Yanzu

Matsalar masu buga mata tsakiya Liberpool ta samu sauye-sauye da yawa a fannin masu taka mata wasa daga tsakiya, bayan da wasu daga ciki suka bar kungiyar, ya dace a ce ta hada

fitattun da za ta fuskanci kakar bana.

Liberpool ta dauki Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen, amma har yanzu dan wasan bai nuna kansa ba, inda yake ta shan suka daga magoya bayan da suke ganin kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba.

Raunin ‘yanwasa da ke jinya

Raunin da wasu ‘yanwasan Liberpool suka ji sun taka rawar gani da kungiyar Liberpool ke kasa kokari a kakar nan. Daga ciki mai tsaron baya, Giobanni Leoni ya ji rauni a wasansa na farko a kungiyar, wanda ake cewa yana doguwar jinya. Mai tsaron raga Alisson Becker ya ji rauni a lokacin gasar zakarun turai wanda ake cewar zai yi jinya har karshen watan Oktoba, watakila ya wuce hakan.

Bayan Liberpool na yoyo

A kakar bara bayan Liberpool ya yi yoyo, duk da cewar kungiyar ce ta lashe kofin, amma dai an samu matsaloli da yawa a bayan. Kungiyoyi da dama sun amfana da kurakuren Liberpool a bara daga ciki har da Nottingham Forest da Brighton da kuma Brentford.

Wasu lokutan da zarar Liberpool ta kai kora sai kaga wagegen gibi tsakanin masu tsare baya da ‘yan tsakiya. Haka kuma tun kafin fara kakar bana, Liberpool ta buga wasannin atisaye, kuma tun a lokacin gurbin masu tsare baya ya nuna matasalar da kungiyar za ta iya fuskanta da fara

kakar nan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025 Wasanni Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray October 30, 2025 Wasanni Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi October 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda