Ta ce: “Kotu ba ta bayar da umarni ba? Ba ku da ikon karɓe fasfona.”

Ba a bayyana wata hujja ko dalili a hukumance ba kan dalilin karɓe fasfo ɗin nata ba, lamarin da ya sa wasu suka zargi cewa ana shirya mata maƙarƙashiya irin ta siyasa.

An hangi mijinta, Cif Uduaghan, yana kiran waya cikin sauri yayin da lamarin ya ɗauki lokaci.

Bayan ‘yan mintuna, jami’an sun mayar mata da fasfo ɗin ba tare da wani bayani ba.

An bar ta ta shiga jirgin kafin ya tashi.

Wasu daga cikin fasinjojin da suka shaida lamarin sun bayyana abin a matsayin abin kunya, inda suke kallon lamarin a matsayin amfani da ƙarfi ba bisa ƙa’ida ba.

Har yanzu, hukumar shige da fice ta ƙasa da ofishin Shugaban Majalisar Dattawa ba su ce komai ba game da lamarin ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Hukumar Shige Da Fice

এছাড়াও পড়ুন:

Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa

Matukar ba a sami sauyin tsare-tsare ba, akwai yiwuwar Ministan Jinkai da Yaki da Talauci, Farfesa Nentawe Yilwatda ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na kasa a yau Alhamis.

Majiyoyi da dama a daren jiya sun shaida wa Aminiya cewa Nentawe ne ke kan gaba a cikin mutanen da ake so su dare shugabancin jam’iyyar mai mulki.

Sai dai a cewar wasu majiyoyin, tsohon Gwamnan Jihar Nasarawa, Sanata Umaru Tanko Almakura shi ma na daga cikin wadanda ake duba yiwuwar ba kujerar.

Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno NAFDAC ta gano dakin ajiye kayayyaki makare da sinadaran hada bam a Kano

A daidai lokacin da ya rage ’yan sa’o’i gabanin taron Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar, majiyoyi da dama sun shaida mana cewa shugabancin jam’iyyar, wanda ya kunshi Shugaban Kasa da Gwamnoni sun yanke shawarar takaita neman wanda zai hau kujerar tsakan Nentawe da Almakura.

Nentawe dai dan asalin jihar Filato ne da ke shiyyar Arewa da Tsakiya, yankin da aka tsara zai fitar da shugaban jam’iyyar kafin daga bisani a nada tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, wanda ya ajiye mukaminsa a farkon wannan watan.

To sai dai majiyoyin sun ce an saka sunan Almakura ne a matsayin zabi na biyu.

Tun bayan saukar Ganduje dai ’yan shiyyar Arewa ta Tsakiya ke ta hankoron ganin an dawo da kujerar yankinsu, kasancewar dan cikinsu, wato Sanata Abdullahi Adamu ne ke kanta kafin ya sauka bayan nasarar Shugaba Tinubu a zaben 2023.

Bayanai sun nuna sai da aka yi dogon nazari kafin a yanke shawarar dauko dan yankin kuma Kirista, saboda a hakurkurtar da wadanda zabin Musulmai guda biyu, Tinubu da Kashim, ya bakantawa.

Duk wanda ya yi nasarar dai shi ne zai karbi ragamar da shugabanta na riko na yanzu, Ali Bukar Dalori, wanda mataimakin shugaba ne kafin saukar Ganduje.

Wasu dai na cewa da shi aka kyale ya ci gaba, amma wata majiyar ta ce kasancewarsa daga jiha daya da Kashim sannan kuma Tinubu na so a yi ta ta kare a kan batun shugabancin ya sa dole a zabo wani.

Wata majiyar kuma ta ce, “Tinubu na san wani dan-a-mutun shi ya zama shugaban kamar yadda Abdullahi Adamu ya kasance zamanin Buhari”.

Sauran wadanda a baya aka yi ta rade-radin za su hau kujerar sun hada da Sanata Sani Musa (Neja) da Sanata Salihu Mustapha (Kwara) da Sanata Joshua Dariye (Filato) da Sanata George Akume (Binuwai) da kuma Sanata Abu Ibrahim (Katsina).

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
  • Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul
  • An kashe mata da yara a sabon harin Filato
  • Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo
  • Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato
  • Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa
  • Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai
  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa