Robert Malley: Harin Amurka A Kan Wuraren Nukiliyar Iran Babban Kure Ne
Published: 25th, July 2025 GMT
Tsohon wakilin Amurka na musamman a kan lamurran Iran Robert Malley, ya caccaki gwamnatin Donald Trump game da kai hare-hare kan cibiyoyin nukiliyar Iran, lamarin da ya ce babban kure ne wanda kuma zai haifar da mummunan sakamako.
Robert Malley ya ce; ina tsammanin zabi na soja ba daidai ba ne bisa kowane irin dalili.
Don haka ina tsammanin cewa wannan shi ne zabi na kuskure da Trump ya dauka, in ji Robert Malley a wata hira da tashar labarai ta NBC ta Amurka.
Ya kuma kara da cewa, mutanen da suke tunanin cewa harin da Isra’ila da Amurka suka kaiwa zai haifar da tayar da kayar baya a cikin gida a Iran, shima wani kuren lissafi ne, saboda hare-haren da gwamnatocin kasashen waje ke kai wa ba wai kawai kan cibiyoyin nukiliyar Iran ba ne, har da asibitoci, da kuma kashe fararen hula.
Ya ce wasu abokansa Amurkawa ‘yan asalin kasar Iran gaya masa cewa, Iraniyawa suna kara samun hadin kai da kishin kasa a duk lokacin da aka kaiwa kasarsu farmaki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
Sojojin ruwan Iran sun sanar da cewa, wani jirgin ruwan Amurka na yaki da ya yi kokarin shiga tekun Oman, ya fuskanci gargadi daga sojojin ruwan Iran tare da tilasta masa janyewa.
Da saiyar yau Laraba ne dai jirgin sama mai saukar angulu mallakin sojojin ruwa, ya yi gargadi ga jirgin ruwan na Amurka da a karshe ya tilasta masa janyewa.
Da fari, jirgin ruwan yakin na Amurka ya yi wa jirgin sama mai saukar angulu na Iran barazanar kai masa hari, said ai duk da haka sojojin ruwan na Iran sun ci gaba da yin gargadi ga Amurkawan da su kar su shiga cikin ruwan tekun Oman.
Bayan wannan barazana ne aka aikewa jirgin ruwan Amurkan sako daga dakarun tsaron sararyin samaniyar Iran akan cewa, wannan jirin mai saukar angulu yana da cikakkiyar kariya, don haka wajibi ne ga jirgin ruwan na Amurka mai suna “DDG Fitzgerald ya janye.