Robert Malley: Harin Amurka A Kan Wuraren Nukiliyar Iran Babban Kure Ne
Published: 25th, July 2025 GMT
Tsohon wakilin Amurka na musamman a kan lamurran Iran Robert Malley, ya caccaki gwamnatin Donald Trump game da kai hare-hare kan cibiyoyin nukiliyar Iran, lamarin da ya ce babban kure ne wanda kuma zai haifar da mummunan sakamako.
Robert Malley ya ce; ina tsammanin zabi na soja ba daidai ba ne bisa kowane irin dalili.
Don haka ina tsammanin cewa wannan shi ne zabi na kuskure da Trump ya dauka, in ji Robert Malley a wata hira da tashar labarai ta NBC ta Amurka.
Ya kuma kara da cewa, mutanen da suke tunanin cewa harin da Isra’ila da Amurka suka kaiwa zai haifar da tayar da kayar baya a cikin gida a Iran, shima wani kuren lissafi ne, saboda hare-haren da gwamnatocin kasashen waje ke kai wa ba wai kawai kan cibiyoyin nukiliyar Iran ba ne, har da asibitoci, da kuma kashe fararen hula.
Ya ce wasu abokansa Amurkawa ‘yan asalin kasar Iran gaya masa cewa, Iraniyawa suna kara samun hadin kai da kishin kasa a duk lokacin da aka kaiwa kasarsu farmaki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa za ta ci gaba da shirin gudanar da babban taronta wanda za a yi a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba a Ibadan da ke Jihar Oyo.
Tun da farko, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta hana jam’iyyar gudanar da taron, inda ta ce PDP ta karya dokokinta na cikin gida.
’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDPMai shari’a James Omotosho, wanda ya jagoranci shari’ar, ya umarci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), da kada ta karɓi ko ta wallafa sakamakon taron har sai PDP ta cika dukkanin sharuɗan da doka ta tanada.
Sai dai a cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar da yammacin ranar Juma’a, kakakinta na ƙasa, Debo Ologunagba, ya ce jam’iyyar ba za ta dakatar da shirin gudanar da taron ba.
Ya bayyana hukuncin kotun a matsayin tauye haƙƙin dimokuraɗiyya a Najeriya.
Ologunagba, ya ce hukuncin ba zai hana PDP ci gaba da shirye-shiryenta na zaɓen sabbin shugabanni da za su jagoranci jam’iyyar na tsawon shekaru huɗu masu zuwa ba.
Ya yi nuni da cewa Kotun Ƙoli ta tabbatar da cewa jam’iyyu na da ’yancin tafiyar da harkokinsu na cikin gida.
“PDP na kira ga mambobinta da shugabanni a faɗin ƙasar nan da su kuma ci gaba da shirye-shiryen babban taron jam’iyyar,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa jam’iyyar mai bin doka ce, kuma ta umarci lauyoyinta da su ɗaukaka ƙara game da hukuncin kotun.