An Yanke Hukuncin Kisa Kan Yan MKO A Nan Iran
Published: 27th, July 2025 GMT
Ma’aikatar sharia a nan Tehran ta bada sanarwan yake hukuncin kisa kan mutane biyu mambobi a kungiyar yan ta’adda ta MKO ko wadanda aka fi sani da munafukai.
Kamfanin dillancin larabann Tasnim na JMI ya nakalto majiyar ma’aikatar na cewa mutanen biyu Mahdi Hassani da Behrouz Ehsani, sun yi amfani da makamai wadanda suka hada da gurneti da kuma wasu ind suka kashe mutane fararin hula a dai dai lokacinda ake hargitsi a cikin kasar don tada hankalin mutane da kuma wargaza harkokin tsaro a cikin kasar.
Labarin ya kara da cewa an tabbatar da tare da wata shakka ba suna aiki tare da kungiyar ta MKO wadanda suke adawa da JMI tun ranar kafa ta.
Kungiyar MKO dai it ace babban kungiya wacce take adawa da JMI ta kuma kashe mata manya-manyan malaman addini a farkon nasarar juyinn juya halin musulunci a kasar. Sannan daga baya tare da taimakon gwamnatin kasar Iraki ta yaki JMI a warare da dama. Daga karshe ta maida cibiyarta zuwa kasashen turai da Amurka inda suke samun makudan kudade don kimar da JMI. MKO ta kashe mutanen iran akalla 17000 tun lokacin shekara 1979 ya zuwa yanzu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kiran Cewa; Ina Masu Fafatukar Kare Hakkin Dan Adam Suke A Bala’in Gaza?
Shugaban kasar Iran ya yi kiran cewa: Ina masu fafutukar kare hakkin bil’adama suke a bala’in Gaza?
Shugaban kasar Iran Dr. Masoud Pezeshkian ya jaddada muhimmancin sauya salon tafiyar da gwamnati da kuma karfafa alaka da kasashen da ke makwabtaka da ita, yana mai cewa masu takama da kare hakkin bil’adama suna nuna fuska biyu a aikinsu, inda suka yi shiru kan munanan laifukan da ake yi wa al’ummar Gaza.
A safiyar yau ne shugaba Pezeshkian ya isa ma’aikatar harkokin wajen kasar, inda ya gana da mataimakan ministoci da daraktocin ma’aikatar.
A lokacin da yake jawabi a taron, shugaban ya ce, “Tun da yake dan majalisar shawarar Musulunci bai canza ba, har yanzu shi mutum daya ne, dole ne al’umma su kasance masu jajircewa da kwarewa tare da ci gaba da yin aiki tukuru, sun mika ragamar mulki ga ministoci da gwamnonin larduna, wasu kura-kurai dole ne a gyara su, me yasa gwamna ba zai iya yin abin da shi yake yi ba?”
Pezeshkian ya kara da cewa, “Idan aka bi tsarin manufofin – wato manyan tsare-tsare, kuma aka ba da iko ga wadanda ke cikin wannan fanni, aikin zai ci gaba. Idan kuskure ya faru, dole ne a gyara shi. Daga nan ne yanayin kasar zai inganta.” Dole ne kuma gwamnoni su mika mulki ga shugabannin kananan hukumomi.