Leadership News Hausa:
2025-07-27@18:25:19 GMT

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Published: 27th, July 2025 GMT

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Daga ranar 24 ga wata, zuwa jiya Asabar 26 ga wata, an gudanar da babban taron kasa da kasa, dangane da fasahar rage asarar hatsi a birnin Jinan na kasar Sin, inda a wajen taron aka sanar da sakamakon da kasar Sin ta samu a fannin takaita asarar hatsi.

An bayyana cewa, a bangaren asarar hatsi da a kan samu yayin da ake girbin hatsi da injuna, yawan asarar alkama, da shinkafa, da masara, da aka samu a kasar Sin a shekarar 2024, ya kai kaso 0.

93%, da 1.76%, da kuma 2.06%, adadin da ya ragu da kaso 1% zuwa kaso 2%, bisa na shekarar 2021, ta yadda aka magance asarar hatsin da yawansa ya kai kilo biliyan 25 cikin shekaru 3 da suka gabata.

Kana ta fuskar tinkarar bala’i, da magance tafka hasara sakamakon hakan, kasar Sin ta riga ta gina ingatattun filayen gona da fadinsu ya kai muraba’in kilomita dubu 667. Kana kasar ta dauki gagarumin mataki na haka magudanar ruwa cikin gonaki, ta yadda aka tabbatar da ingancin aikin ban ruwa, da fitar da ruwa a lokacin ambaliya, a cikin fiye da rabin gonakin kasar. Ban da haka, kasar ta karfafa yin gargadin yiwuwar abkuwar cututtukan da suka shafi hatsi, da bala’in kwari, ta yadda ake samu damar rage asarar hatsi da yawansa ya kai fiye da kilo biliyan 140 a duk shekara. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: asarar hatsi

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

A yau Alhamis shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sakon ta’aziyya ga takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin, bisa hadarin jirgin saman fasinja da ya auku a kasar, wanda ya haddasa rasa rayuka da dama.

Kafar dillancin labarai ta “The Russia Today”, ta hakaito kwamitin binciken hadarin na cewa, dukkanin mutanen dake cikin jirgin saman mai lamba An-24 da ya yi hadari a yau Alhamis a yankin Amur na kasar Rasha sun rasu. An ce, jirgin na dauke da fasinjoji 43, da kuma matuka da masu bayar da hidima 6. (Saminu Alhassan)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hanyoyin Gyaran Gashi
  • Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba
  • Jagora: Za’a Gaggauta Ci Gaba A Ilmi Da Fasahar Tsaron Sojojin Kasar
  • Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
  •   New York Times: Harin A Sansanin Udaidai Ya Jaza Wa Amurka Asarar Dala Miliyan 111
  • Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA
  • Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
  • Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
  • Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar