Tawagar ƙwallon ƙafa ta mata a Nijeriya (Super Falcons) za ta buga wasan ƙarshe na gasar kofin ƙasashen Afirika yau da ƙasar Moroko a filin wasa na Olympique da ke birnin Rabat na ƙasar Moroko, za a buga wasan da misalin ƙarfe 9 na dare agogon Nijeriya.

Wannan ne karo na biyu da ƙasashen biyu za su haɗu a tarihi, sun haɗu a karon farko a shekarar 2022 a wasan kusa da na ƙarshe na gasar kofin ƙasashen Afirika na mata, inda Moroko ta fitar da Nijeriya bayan bugun Fenarati, a wannan karon duka ƙasashen biyu na daga cikin waɗanda ake hasashen za su iya lashe kofin, duba da cewa babu kanwar lasa a cikinsu.

Kano Pillars: Yaushe Kungiyoyin Kwallon Nijeriya Za Su Daina Shiga Matsalar Kudi? Kwallon Mata: Nijeriya Ta Nuna Wa Afrika Ta Kudu Kwanji A Pretoria

Idan Nijeriya ta samu nasarar lashe kofin zai kasance karo na 10 kenan da ta lashe kofin a tarihi, idan kuma Moroko ce ta yi nasara zai kasance na farko da ƙasar ta Arewacin Afirika ta taɓa lashewa, hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirika (CAF) za ta bai wa duk wanda ya lashe gasar zunzurutun kuɗi har Dala miliyan 1, yayin da wanda ya zo na biyu zai samu Dala 500,000.

Tsohon kocin Sifaniya Jorge Vilda ke jagorantar tawagar Moroko, yayin da Justin Madugu ke jagorantar Nijeriya, wadda ke kan gaba wajen iya taka leda a nahiyar, ta samu nasarar doke Afrika ta Kudu mai riƙe da kofin gasar a yayin da Moroko ta fitar da ƙasar Ghana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ƙwallon mata Nijeriya WAFCON 2025

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Jarida Da Suka yi Shahada A Gaza Sun Kai 232, Yayin Da Wadanda Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Yunwa Suka Kai 122

‘Yan jarida akalla 232 suka yi shahada sannan wasu 122 sun rasa rayukansu sabaoda masifar yunwa a yankin Zirin Gaza!

Yakin kisan kare dangi da ake yi a zirin Gaza yana ci gaba da lakume rayukan Falasdinawa da dama a kowace rana, manya da kanana…ta hanyar jefa bama-bamai, kisa, killace yankin da kakaba masifar yunwa.

A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, an kashe Falasdinawa da dama tare da jikkata wasu daruruwa, ciki har da masu neman agaji, sakamakon hare-haren da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan wata makaranta da ke dauke da ‘yan gudun hijira a unguwar al-Rimal da gidaje da sansanonin ‘yan gudun hijira a yankunan al-Amal, al-Tuffah, da al-Nasr, dake gabashi, arewacin Gaza.

Hakazalika an sha kai hare-hare ta sama a yankunan al-Balad da al-Amal da ke Khan Yunus da ke kudancin zirin Gaza, da kuma harin bama-bamai da jiragen yakin sojin mamayar Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu
  • Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko
  • Yadda Hadarin Mutuwa Ke Karuwa Yayin Ko Bayan Saduwa Da Iyali
  • Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu  A Kaduna
  • Wani mutum ya buɗe Ofishin Jakadancin Indiya na bogi a ƙasar
  • Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
  • ‘Yan Jarida Da Suka yi Shahada A Gaza Sun Kai 232, Yayin Da Wadanda Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Yunwa Suka Kai 122
  • Tinubu ya fi mayar da hankali wajen gina Kudancin Nijeriya — Kwankwaso
  • Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja