Leadership News Hausa:
2025-11-03@04:03:12 GMT

Hanyoyin Gyaran Gashi

Published: 27th, July 2025 GMT

Hanyoyin Gyaran Gashi

Amfani da man kwakwa da man Amla: Daga farko ki dora man kwakwa a wuta sannan sai ki zuba masa man Amla. Daga nan sai ki gauraya sosai, idan kin tabbata sun gaurayu, sai ki sauke daga wuta, har hadin ya huce. Sannan ki zuba man a kwalba kina shafa wannan hadin a fatar kanki da gashinki kamar sau uku a sati.

Amfani da Lemon Tsami: Ki samu ruwan Lemun Tsami, sai ki hada shi da kwai da kuma man Amla. Sai ki shafa hadin a fatar kai da kuma gashi. Ki bar hadin a kanki har tsawon minti talatin, sannan ki wanke da ruwan Dumi. Za ki iya yin wannan hadin sau biyu a wata.

Amfani da Alo Bera: Ki samu ruwan Alo Bera, sai ki shafa a fatar kai da kuma gashi, bayan minti ashirin sai ki wanke da ruwan dumi.

Amfani da man Zaitun: Man zaitun na sanya gashi ya yi baki, taushi da kuma tsawo. Za ki iya mayar da man zaitun ya zama man kitsonki.

 

Hanyoyin karin tsawon gashi

Amfani da danyen kwai:

Kayan hadi:

Danyen Kwai. Roba mai Kyau mai dan fadi

Ki samu wannan kwan naki sai ki dauko wannan roba taki sannan ki fasa wannan kwan sai ki cire kwanduwar kwan ma’ ana wannan yallon abin na ciki ki ajiye gefe daya, sai ki juye farin ruwan kwan a wannan roba taki. Idan gashin naki da dan yawane sai ki fasa kwan kamar uku-kodai yada ya samu. Sannan ki dinga diban wannan farin ruwan kwan kina shafe shi a gashin naki, har sai kin tabbatar cewa ruwan kwan ya ratsa ko ina cikin gashin naki.

Saiki bar shi tsawon mintuna ashirin ko talatin sai ki wanke kan naki da sabulu mai kyau kina iya amfani da sabulun Alo Bera. Kada kimanta cewa gashi ya kan sanya mazaje kara kaunar matayensu .

 

Amfani da man Amla:

Abubuwan da za a bukata: Man Amla, Zuma, Ruwan dumi. A zuba cokalin Amla biyu a roba, sannan sai a zuba rabin cokalin zuma a cikin Amla, a sanya cokalin ruwan dumi kamar biyu zuwa uku, sannan sai a juya hadin har sai sun cakudu da juna, daga nan a taje gashi kamin a shafa wannan hadin a fatar kai.

A jira na tsawon mintuna talatin, daga nan sai a wanke kai da man wanke gashi (shampoo).

 

Maganin bushewar gashi

Amfani da ayaba: Kayan hadi : Zuma cokali daya, Nunanniyar Ayaba, za ki bare bawon Ayaba sai ki markada a injin nika (blender ) ta markadu sosai .

 

Ki zuba zuma cokali daya ki gauraya su su hadu , sannan ki shafa a gashi tun daga karkashinsa har baki. Ki rufe kan da hular leda (shower cap). Bayan mintuna sha biyar zuwa ashirin sai ki wanke kan da sabulun wanke gashi (Shampoo ) da na karawa gashi maiko (conditioner ).

 

wannan ita ce hanya mafi sauki kuma mafi kawo sakamako mai kyau.

 

Kwabin Kwanduwar kwai da Fiya (Abocado ) 

Kayan hadi:

Kwanduwar kwai, Fiya

 

Ga yadda ake hadawa

 

Za ki bare Fiya, sai ki zuba a injin markade, ki zuba kwanduwar kwan ki a kai sai ki markada sannan ki shafa a gashinki tun daga karkashin sa har baki. Ki samu hular leda ki rufe kan da shi.

 

Ap Oil, Man Shafawa 

 

Yadda za ki hada asamu manshafawa mafi kankanta wato mai araha sai a juye kwalbar ap oil gaba daya sai a sami wani abu a juya sosai sai a rufe bakin tsawon minti biyu (2) ko uku ( 3 ) shikenan ya hadu.

 

Dokokin amfani da shi:

 

Mutane 2 Ba sa Tabawa Ba a barinsa a bude. Ba a amfani da manshafawa mai tsada sai ( Local One) Ba a sawa da rana sai gari ya yi huhu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka

A yayin da ake ci gaba da cece-kuce kan kalaman Shugaban Amurka Donald Trump da ke zargin gwamnatin Nijeriya da watsi da batun kisan Kiristoci a ƙasar, Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta bayyana cewa ta fara shirin kai farmaki a Nijeriya.

Sakataren Ma’aikatar, Pete Hegseth, ne ya tabbatar da hakan cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, yana mai cewa ma’aikatarsa “na shirye-shiryen ɗaukar mataki” bayan umarnin da Trump ya bayar.

Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 

“Muna shirye-shirye don ɗaukar mataki a Nijeriya. Idan gwamnatin Nijeriya ba ta kare Kiristoci ba, za mu kai hari, mu kawar da ‘yan ta’addan Musulmai da ke aikata wannan ta’asar,” in ji Hegseth.

Trump dai ya yi wannan barazanar ne a cikin wani saƙo da ya wallafa a Truth Social, inda ya ce Amurka za ta dakatar da duk tallafin da take bai wa Nijeriya, kuma tana iya “shiga ƙasar da ƙarfin soji domin share ‘yan ta’addan da ke kashe Kiristoci.”

“Idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da duk wata tallafi, kuma mai yiwuwa ta shiga wannan ƙasar, ta cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ’yan ta’addan Musulmai masu zafin kishin addini,” in ji Trump.

Ya kuma gargaɗi gwamnatin Nijeriya da ta gaggauta ɗaukar mataki, yana cewa idan Amurka ta kai farmaki “za ta yi shi cikin sauri, da tsananin ƙarfi, da gamsuwa.”

Lamarin na zuwa ne kwana guda bayan Trump ya mayar da Nijeriya cikin jerin ƙasashen da za a sanyawa ido, yana zargin cewa “ana yi wa Kiristoci kisan gilla” a hannun ƙungiyoyin Musulmi masu tsattsauran ra’ayi.

Sai dai a martanin da ya mayar, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce Nijeriya tana nan daram a matsayin ƙasa mai dimokuraɗiyya wadda kundin tsarin mulkinta ke tabbatar da ‘yancin yin addini da haƙuri tsakanin mabambantan addinai.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatinmu tana gudanar da tattaunawa sosai da shugabannin addinai na Kiristanci da Musulunci, tare da ci gaba da magance matsalolin tsaro da ke shafar ‘yan ƙasa daga addinai da yankuna daban-daban,” in ji Tinubu.

A cewar mai ba wa Tinubun shawara na musamman kan yaɗa manufofi, Daniel Bwala, za a yi ganawa tsakanin Shugaba Tinubu da Shugaba Trump “a cikin kwanaki kaɗan masu zuwa” domin tattaunawa da warware wannan saɓanin fahimta.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • Yadda Za Ku Hada Fab Biskit
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC