Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Published: 27th, July 2025 GMT
Idan aka aiwatar da wannan aiki yadda ya kamata, zai iya zama abin koyi a tsarin samar da gidaje a Nijeriya. Amma in aka bar shi ya faɗa cikin halin almubazzaranci da rashin kulawa da ya jima yana faruwa, to zai iya zama wani sabon abin misalin da ba zai amfani talaka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 3.5 Wajen Gina Shaguna A Farm Centre
Gwamnatin Jihar Jigawa ta fara aikin gina shaguna guda dubu daya a cibiyar kasuwanci ta Farm Centre da ke Kano, wanda zai lakume kudi Naira Biliyan Uku da rabi (N3.5bn), domin bunkasa kudaden shiga na cikin gida na jihar.
Shugaban Kungiyar Hadaka kan Tsaro, Zaman Lafiya da Warware Rikice-rikice a Jihar Jigawa, Muhammad Musbahu Basirka, ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a sakatariyar NUJ da ke Dutse, babban birnin jihar.
Ya bayyana cewa, hukumar EFCC ce ta mika filin hannun gwamnatin jihar Jigawa a matsayin wani bangare na dawo da kadarorin da jihar ta gada daga tsohuwar jihar Kano.
Ya ce: “Wannan fili da ke a tsakiyar birnin Kano, na daga cikin kadarorin da jihar Jigawa ta gada bisa tsarin raba kadarori da filaye da aka yi bayan kirkar jihar Jigawa daga tsohuwar jihar Kano a watan Agustan 1991.”
“Bayan tattaunawa da masana, shugabannin al’umma da kuma masu ruwa da tsaki, muna sanar da jama’ar jihar Jigawa cewa gwamnatinmu ta yanke shawarar amfani da wannan fili mai muhimmanci domin amfanar kowa da kowa.”
“Manufar ita ce kara habaka kudaden shiga na cikin gida na jihar, kasancewar filin na dag cikin muhimman wuraren kasuwanci na Kano. Gwamnatinmu na fuskantar bukatar fadada hanyoyin samun kudaden shiga ba tare da dogaro kacokan ga kasafin kudi na kasa”.
Yayin da ya ke kira ga ‘yan asalin jihar da sauran mazauna da su rungumi wannan cigaba da fahimta da hadin kai, Musbahu Basirka ya ja hankalin jama’a da a guji siyasantar da wannan lamarin.
“Duk da haka muna maraba da shawarwari masu amfani kan hanyoyin da za a fi amfana da wannan aiki mai matukar muhimmanci domin dorewar ci gaba ga al’umma.” In ji shi.
“Mu a matsayinmu na wakilan kungiyoyin fararen hula, za mu kasance cikin tsaka-tsaki wajen sa ido da tabbatar da cewa an yi aiki mai inganci, tare da yin nazari lokaci-lokaci domin tabbatar da gaskiya da adalci ” in ji Basirka.
Usman Muhammad Zaria