Sojoji sun ceto yaro da aka sayar shekaru 3 a Filato
Published: 25th, July 2025 GMT
Dakarun Runduna ta 3 ta ‘Operation Safe Haven’ masu wanzar da zaman lafiya a Jihar Filato sun ceto wani yaro ɗan shekara 12 a Ƙaramar hukumar Riyom da ke jihar.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Manjo Samson Zhakom ne ya bayyana hakan a hedikwatar rundunar yayin da yake zantawa da manema labarai a ranar Juma’a.
A cewar rundunar, kawun yaron ne ya sayar da shi shekaru uku da suka wuce.
Rundunar ta ce, an kuɓutar da yaron ne bayan wani samame da sojoji suka kai a maɓoyar miyagun da ke a Ƙaramar hukumar Riyom.
Da yake bayyana yadda aka kuɓutar da yaron, Manjo Zhakom ya ce “a ranar 22 ga Yuli, 2025, sojoji sun ceto wani yaro ɗan shekara 12 a lokacin da suka kai samame a maɓoyar ‘yan ta’adda a yankin Riyom.
“Bincike ya nuna cewa, kawunsa ne ya siyar da yaron shekaru 3 da suka gabata, amma an miƙa yaron ga Kansila mai wakiltar mazaɓar Zamko na Ƙaramar hukumar Langtang ta Arewa a jihar Filato, wanda ake sa ran zai miƙa yaron ga danginsa,” in ji kakakin.
A wani labarin makamancin haka, rundunar ta ce dakarun sojin sun ƙwato makamai da alburusai a wani samame da suka kai a Ƙaramar hukumar Wase da ke jihar.
Manjo Zhakom ya bayyana cewa, “Bisa ga sahihan bayanan sirri da suka gano, ‘yan bindiga ɗauke da bindigogi ƙirar AK-47 a kan titin Kampani zuwa Kombodoro a Ƙaramar hukumar Wase ta Jihar Filato, sojojin sun yi kwanton ɓauna a kan hanyoyin ’yan fashi da ke kusa da unguwar Jeb.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: a Ƙaramar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
’Yan sanda a jihar Legas sun kama wani tsohon fursuna tare da wasu mutum biyu bisa zargin hannu a jerin laifukan fashi da yankan aljihu a jihar kwana biyar da fitowa daga kurkuku.
Tsohon fursunan mai shekaru 25 da haihuwa, Segun Kolawole, an kama shi ne bayan kwana biyar da aka sako shi daga cibiyar gyaran hali ta Kirikiri, a jihar Legas.
Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano SpalletiSauran wadanda aka kama tare da shi sun haɗa da Sodiq Isa mai shekaru 27 da Adekanmbi Ganiu mai shekaru 21.
Rahotanni sun nuna cewa an kama waɗanda ake zargin ne bisa laifukan yankan aljihun mutane da sauran laifukan sata a sassa daban-daban na jihar.
Mai magana da yawun ’yan sandan jihar, SP Abimbola Adebisi, ta tabbatar da cafke Kolawole, inda ta ce an kama shi da misalin ƙarfe 8 na safiyar Talata a kasuwar Oshodi, bayan jami’ai sun lura da motsinsa da ya zama abin zargi.
Adebisi ta ce an same shi da tsabar kuɗi ₦80,000 da wayar Infinix Note 40 Pro, waɗanda aka gano daga wani fashi da ya aikata a Opebi, inda ake zargin ya saci ₦200,000 da wayar daga hannun wani ɗan kasuwa da ke barci.
“Bincike ya ƙara tabbatar da cewa ya riga ya sayi sabbin kaya da takalma da wani ɓangare na kuɗin da ya sata, waɗanda suma aka kwato su daga hannunsa,” in ji ta.
Haka kuma, a wani samame daban da aka gudanar da misalin ƙarfe 5 na yamma a ranar Juma’a, jami’an RRS sun kama Sodiq Isa da Adekanmbi Ganiu bisa zargin yunkurin satar wayoyin hannu daga hannun fasinjoji a sassa daban-daban na Legas.