Aminiya:
2025-07-25@21:26:00 GMT

Ruwa da iska sun kashe mutum, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe

Published: 24th, July 2025 GMT

Ruwan sama kamar da bakin kwarya hade da iska sun yi ajalin mutum biyar sannan wasu 92 suka samu munanan raunuka a kananan hukumomi bakwai na jihar Yobe.

Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (SEMA) Dr Goje ne ya tabbatar da hakan a ranar Laraba a Damaturu.

Ya ce iftila’in ya shafi al’ummomi 48 ne a fadin kananan hukumomin da lamarin ya faru.

Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace

Dr Goje yan kuma ce bala’in ya shafi gidaje 1,264, tare da raba mutum 5,022 da muhallansu.

Shugaban ya kuma ce hukumarsa tare da hadin gwiwar kungiyar bayar da tallafi ta kasa da kasa ACF tare da tallafi daga ofishin kula da harkokin wajen Jamus (GFFO), sun raba kayan agajin ceton rai ga magidanta 566 a kananan hukumomin Fika da Potiskum da lamarin ya shafa.

Kazalika, kididdigar haɗin gwiwa ta hukumar ta SEMA da ACF suka fitar ta ba da fifiko ga iyalan da wadanda wannan iftila’i ya fi shafa kai tsaye musamman waɗanda suka rasa gidajensu, da kayan masarufi, ko damar samun wani taimakon na tsafta.

Mohammed Liman Kingimi, na kungiyar ACF, ya tabbatar da kudurin kungiyar na kara ba da taimako bisa ga yadda bukatun hakan suka taso.

Ya ce kungiyar na kuma shirye-shiryen kaddamar da tallafin abinci ga magidanta 566 don rage musu radadi.

Dokta Goje ya buqaci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da shi yadda ya kamata sannan ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na kare al’umma masu rauni ta hanyar xaukar matakan gaggawa.

Ya kuma jaddada qudirin hukumar cewa kullum a shirye take wajen gudanar da ayyukanta kamar yadda ya dace.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ruwa da iska

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar “Human Right Watch” Ta Yi Kira Da A Saki Tsohon Shugaban Kasar Nijar Muammad Bazoum

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Human Right Watch” ta yi kira ga gwamnatin sojan jamhuriyar Nijar da ta saki tsohon shugaban kasar Muhamad Bazum, wanda ake tsare da shi tun lokacin juyin mulkin watan Yuli na 2023.

Kungiyar ta kuma ce, ci gaba da tsare Muhammad Bazum da ake yi ba tare da yi masa shari’a ba, ya sabawa doka da kuma take dokokin kasa da kasa na sharia.

 Bayan juyin mulkin na 2023, shugabannin soja sun yi alkawalin gabatar da Bazum a gaban kotu domin yi masa shari’a bisa zargin cin amanar aksa.

A 2024, kotun musamman da aka kafa ta cirewa tsohon shugaban kasar rigar kariya, da hakan ya zama tamkar share fage domin yi masa sharia,sai dai har yanzu hakna ba ta faru ba.

Lauyoyin da suke bai wa Bazzoum kariya sun nemi taimakon kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada MDD da kungiyar tattalin arziki ta yammacin Afirka ( ECOWAS).

Dukkanin kungiyoyin na kasa da kasa da kuma na yammacin Afirka sun sha yin kira da a saki Bazzum ba tare da wani sharadi ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Tawayen Sudan Ta Kungiyar Rapid Support Forces Sun Kashe Mutane 27 A Yammacin Jihar Kordofan Ta Kasar Sudan
  • Gwamnatin Yobe ta bada tallafi ga iyalan ’yan banga da suka rasu
  • Kungiyar “Human Right Watch” Ta Yi Kira Da A Saki Tsohon Shugaban Kasar Nijar Muammad Bazoum
  • Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Ɓullar Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan sama da mutum 100
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan mutum sama da 100
  • NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe