Kakakin rundunar tsaron Isra’ila ya ce suna aiki tare da la’akari da dokokin duniya, inda ya ce Hamas na boye “makamai” a cikin fararen hula, sannan suna “rusa gine-gine ne kawai idan ta zama dole.”

An gani a zahiri yadda Rafah ya lalace a kusa da bakin iyakar Masar

A ‘yan makonnin da suka wuce, sojojin Isra’ila da ‘yan kwangilar rusau sun sanya alamar rusau a gidaje da dama

Nazarin masa irin su Corey Scher da Jamon Ban Den Hoek ya nuna cewa barnar da aka yi a Gaza tun daga watan Afrilu ya yi muni a yankin.

 

Akwai manyan motocin katafila jigbe a yankunan

A watan Yuli, ministan tsaron Isra’ila, Katz ya bayyana tsare-tsarensu na kafa abin da ya kira “birnin aikin ceto” a Rafah, inda za a fara da ajiye Falasdinawa 600,000 a sansanin.

Yunkurin na shan suka sosai. Tsohon firaministan kasar, Ehud Olmert ya shaida wa BBC cewa tsarin zai yi kama “kafa sansanin ajiye wadanda ba a so.”

Tel al-Sultan na cikin biranen da suka fi yawan mutane a yankin Rafah. Akwai tarin mutane kuma a garin ne asibitin kula da yara da marayu da yaran da aka tsinta suke rayuwa.

Hotunan tauraron dan’adam da ke nuna yadda hare-haren sojojin Isra’ila ya barnata yankin duk da akwai gomman gine-gine da suka tsira.

Zuwa ranar 13 ga Yuli, hare-haren sun riga sun munana, inda ake samun manyan gine-gine sun rufta baki daya. Asibitin na cikin ‘yan tsirarun gine-ginen da suka rage.|| Haka kuma an sanya alamar rusau a gine-ginen da ke kusa da garin Saudi – garin da ke dauke da babban masallaci da makarantu da dama.

Wani faifan bidiyo da aka tabbatar ya nuna wata tanka na tafiya a titin Rafah wasu ma’aikata kuma suna diga.

Haka kuma Isra’ila ta yi rusau a wasu sassan zirin wadanda suka tsira daga hare-haren farko.

Birnin Khuza’a da ya yi fice da noma, wanda ke da da nisan kilomita 1.5 (mil 0.9) daga bakin iyakar Isra’ila.

Kafin fara yakin, birnin na da mutum 11,000, kuma yana da kasar noma mai kyau da ake noma tumatir da fulawa.

Rundunar sojin Isra’ila ta ce ta rusa gine-gine 1,200 a Khuza’a, wadanda ta yi zargin kadarorin “‘yanta’adda” ne da Hamas ke amfani da su.

An samu labarai irin haka a birnin Abasan al-Kabira, inda kusan mutum 27,000 ke rayuwa kafin yakin. Hotunan da aka dauka a 31 ga Mayu da 8 ga watan Yulin sun nuna yadda aka daidaita yankin a cikin kwana 38.

Isra’ila ta kirkiri “sansanonin tsaro” a tsakanin wasu yankunan Gaza, kuma ta lalata gine-gine da dama a tsakanin su. Wurin da ta kai farmaki na kusa-kusan nan shi ne gab da gabashin Khan Younis, ciki har da Khuza’a da Abasan al-Kabira.

Haka kuma tun farkon yakin, masana suke hasashen Isra’ila na yunkurin kafa “cibiyoyin tudun mun tsira” ta hanyar rusa gine-gine da ke gab da bakin iyakarta.

A Kizan Abu Rashwan – yankin da ya yi fice da noma mai nisan kusan kilomita 7 daga bakin iyakar Isra’ila – kusan kowane gini da ke tsaye an rusa shi daga ranar 17 ga Mayu.

Sashen BBC Berify ya gabatar da sakamakon bincikensa ga IDF ciki har da wuraren da ta rusa, inda aka bukaci ta yi bayani, amma ba ta yi ba.

“Kamar yadda aka sani ne, Hamas da sauran kungiyoyin ‘yanta’adda na boye makamai a cikin fararen hula,” in ji kakakin IDF. Sannan ya kara da cewa IDF na “ganowa tare da barnata kadarorin ‘yanta’adda da suke cikin gine-ginen ne.”

Lauyoyin kare hakkin dan’adam da dama da BBC Berify ta zanta da su sun ce akwai alamun Isra’ila ta aikata laifukan yaki.

Eitan Diamond – wani babban lauya da ke aiki a cibiyar agaji ta Diakonia International Humanitarian Law Centre da ke Jerusalem – ya ce akwai ‘yar hujja da ta kafe da shi a cikin yarjejeniyar Geneba ta hudu.

“Dokokin duniya sun haramta wadannan mamayar da barnata kadarorin fararen hula a lokacin yaki, sai dai idan ya matukar zama dole,” in ji Mr Diamond said.

“Amma barnata kadarori saboda kawai zargin yiwuwar za a yi amfani da su a gaba ba ya cikin uzurin da aka tsara a yarjejeniyar.”

Farfesa Janina Dill, darakta a cibiyar shari’a da yaki ta Odford Institute for Ethics, Law & Armed Conflict ta ce kasar da ta yi mamayar dole ta killace wani yankin domin kare wasu mutane – wadda ta ce ba zai yiwu a yi amfani da karfin soji ba.”

Amma wasu masanan sun kare rundunar IDF.

Gine-gine da dama da IDF ta rusa sun zama kufai, “in ji Farfesa Eitan Shamir, darakta a cibiyar BESA Center For Strategic Studies da ke Isra’ila kuma tsohon jami’i a ma’aikatar tsare-tsare. Ya bayyana wa BBC Berify cewa gine-gine sun barazana ga masu komawa garuruwan su saboda za su iya rushewa a kowane lokaci”.

Haka kuma Farfesa Shamir ya ce akwai rashin tsari.

“Wuraren sun zama na yaki,” in ji shi. “Ko da ma IDF ta mamaye wurin, da zarar Isra’ila ta janye, mayakan suna komawa su dasa bama-bamai ko su boye a ciki.”

Babu alamar janyewa a yunkurin na rusau. Kafofin watsa labarai na Isra’ila sun ce IDF ta dauko manyan katafila da ake kira D9 daga Amurka.

Kuma sashen BBC na BBC Berify ya gano gomman tallata guraban aiki da aka watsa a zaurukan Facebook na ‘yan Isra’ila da ake neman ma’aikata da za su yi aikin rusau a Gaza, wadanda aka rika yadawa tun a watan Mayu.

Wasu rubuce-rubucen sun bayyana wuraren da za a yi aikin a Gaza kamar “yankin Philadelphi” da “yankin Morag” – duk a karkarshin IDF.

Da BBC Berify ya tuntubi wani dan kwangila, sai ya ce, “ka je (wasu maganganu) da kai da Gaza.”

Wani masani – Adil Hakue na tsangayar shari’a ta Rutgers – ya yi hasashen rushe-rushen IDF ba za su rasa nasaba ba da yunkurin kafa “yankin soji” da za ta “mamaye daga baya” ba.

Wasu masana kuma sun ce rusau din share fage ne domin kafa “cibiyar agaji” a Rafah – Shugaban cibiyar nazarin tsaro da tsare-tsare ta Institute for Strategy and Security da ke Jerusalem – ya ce watakila suna so ne su tursasa wa Falasdina barin zirin baki daya.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya taba bayyana wa a baya a wani taro da ‘yan majalisa cikin sirri cewa IDF za ta rusa gine-gine ne domin ya zama Falasdina ba su da wurin komawa”.

Amma a wajen ‘yan Gaza, matsala cebabb.a.

Moataz Yousef Ahmed Al-Absi daga Tel al-Sultan ya ce an mayar da gidansa kufai.

“na koma gidan ne kimanin shekara biyu kafin a fara yakin, inda nake tsammanin zan cigaba da rayuwa. Amma yanzu ya zama kufai,” in ji shi.

“Na rasa komai, yanzu ban san yadda zan yi ba.”

 

Kungiyoyin agaji sun bukaci a gaggauta tsagaita wuta a Gaza

Kungiyoyi agaji fiye da dari sun yi gargadin yaduwar mummunar yunwa a Gaza, inda mutane fiye da miliyan biyu ba su iya samun abinci.

Kungiyoyin sun ce a halin da ake ciki yanzu hatta ma’aikatansu su na fama da karancin abinci a Gaza.

Kungiyoyin agajin da suka fitar da rahoton mawuyacin halin da mutane ke ciki a Gaza sun hada da kungiyar likitoci ta kasa da kasa, da Sabe the Children da kuma Odfam.

Sun ce ma’aikatansu ba su da wani zabi illa su shiga layin neman agajin abinci tare da al’umma Gaza, wani abu da ke sanya su shiga yanayin da za a iya harbe su, saboda kokarin nema wa iyalansu abinci.

Sun bukaci a samar da tsarin rabon kayan agaji a Gaza ta hannun hukumomin Majalisar Dinkin Duniya.

Isra’ila ta amsa cewa an samu raguwa da gagarumin rinjaye kan yawan kayan agaji da Falasdinawa ke samu, amma ta musanta cewa akwai yunwa a yankin.

Dr Graeme Groom babban likitan kashi ne a asibitin London, wanda kuma ya yi aiki a Gaza a watan jiya.

Ya ce: ”A kullum abokan aiki na aiko mani sako domin sanar da ni cewa babu abinci. Kwanaki biyu da suka wuce, wani babban jami’in mu ya shaida mani cewa babu abinci, kuma ko kadan babu, sai ya ce ai babu komai, asali ma cikin matsananciyar yunwa suke.”

Wani rahoton da ma’aikatar lafiya ta Hamas ta fitar ya ce mutane fiye da 30 suka mutu saboda tsananain yunwa a kanaki uku, lamarin da Isra’ila ta ce farfaganda ce kawai.

Kungiyoyin sun bukaci a gagauta kawo karshen yakin domin samun damar shigar da wadataccen abinci ga al’ummar Gaza.

Mun Ciro Wannan Rahoto Daga BBC Hausa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Ba Da Agajin Jin Kai Ta ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinawa Ta “UNRWA” Ta Sanar Da Kashe Ma’aikatan 330 A Gaza

Hukumar ba da agaji da kula da ‘yan gudun hijirar Falasdinawa ta “UNRWA” tana karkashin wuta sakamakon ma’aikatan 330 da suka yi shahada kuma aka lalata cibiyoyinta 300 a Gaza!

Inas Hamdan, mai magana da yawun hukumar ta UNRWA a birnin Alkahira, ta tabbatar da cewa; Yunwar da ke faruwa a zirin Gaza, wani bala’i ne da ba a taba ganin irinsa ba, wanda ya shafi mutane sama da miliyan biyu, ciki har da akalla yara miliyan daya. Wannan ya saba wa duk dokokin jin kai da ka’idoji, kuma abin takaici, lamarin yana da kara muni.

Hamdan ta yi nuni da cewa, a lokacin da suke magana kan matsalar agajin jin kai ko shigar da kayan abinci zuwa zirin Gaza, suna fuskantar shamaki da aka sanya a zirin Gaza, baya ga tsarin rabon da wata gidauniya mai suna Gazan Humanitarian Foundation ke gudanarwa, wanda ke zama tarkon mutuwa. Ya zuwa yanzu, fiye da mutane dubu sun mutu yayin da suke jiran abinci, haƙƙin duk mazauna cikin wannan mawuyacin yanayi.

Ta yi gargadin cewa matakan karancin abinci na ci gaba da tabarbarewa, inda ya kai matakin da ba a taba ganin irinsa ba da kuma matukar damuwa. Adadin matsalolin rashin abinci mai gina jiki, musamman a tsakanin yara, yana nuna mummunar tabarbarewa a wannan fanni. Akalla yara 5,500 ‘yan kasa da shekaru biyar ne ke fama da matsananciyar rashin abinci mai gina jiki, ciki har da yara akalla 800 da ke cikin matsanancin hali na rashin abinci mai gina jiki, ma’ana suna fuskantar barazanar yunwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Gaza: Ana Ci Gaba Da Samun Shahidai Da Yunwa Take Kashewa A Gaza
  • ‘Yan Jarida Da Suka yi Shahada A Gaza Sun Kai 232, Yayin Da Wadanda Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Yunwa Suka Kai 122
  • Miliyoyin Al’ummar Yemen Sun Fito Taron Gangamin Nuna Goyon Baya Ga Falasdinawa
  • Hukumar Ba Da Agajin Jin Kai Ta ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinawa Ta “UNRWA” Ta Sanar Da Kashe Ma’aikatan 330 A Gaza
  • Iran da Bangladesh sun bukaci taron gaggawa na OIC kan kisan kiyashi a Gaza
  • Fiye Da  Falasdinawa 111 Ne Su Ka Yi Shahada Saboda Yunwa A Gaza
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Fara Tattaunawa kan Masifar Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Asusun Kula Da Kananan Yara Na Majalisar Dinkin Duniya “UNICEF” Ya Yi Gargadi Kan Bala’in Jin Kai A Gaza
  • Majalisar Dokokin Isra’ila Ta Kada Kuri’ar Sake Mamaye Yankunan Flasdinawa