A jiya Juma’a ne dai wanda ya isa birnin Beirut ya yi kira ga al’ummar kasar da su yi riko da hadin kan kasa da dukkanin bangarorinsu, sannan kuma su ci gaba da zage damtse wajen kalubalantar makiyar kasar Lebanon,musamman ‘yan sahayoniya.

Goerge Ibrahim Abdullah wanda kuma  ya gabatar da taron manema labaru a garinsu na “Qubyat’ ya kara da cewa; Kamar yadda mu ka kasance garkuwa mai bayar da kariya ga kasa, za mu ci gaba da zama haka’ sannan kuma ya kara da cewa: Saboda jinanen Shahidai kasar Lebanon za ta iya kalubalantar dukkanin hatsurran da take fuskanta.

Har ila yau, ya bayyana cewa;sojojin kasar Lebanon suna da mazajen da za su iya kare kasa,illa iyaka abinda ya rage su, shi ne makamai.”

Akan mahaifarsa Gubyat, Goege Abdullah ya ce, a tsawon lokacin garin ya kasance wani alami na hadin kan al’ummar kasar.”

A filin saukar jiragen sama na “Rafiqul-Hariri” dake birnin Beirut, Goerge Ibrahim Abdullah ya sami kyakkyawar tarba daga ‘yan majalisa da jam’iyyun siyasa da kuma mutanen gari da dama.

  A takaitaccen bayanin da ya yi a filin saukar jiragen saman na Beirut, ya sake tabbatar da matsayarsa na ci gaba da riko da gwgawarmaya da goyon bayan al’ummar Falasdinu.

Har ila yau ya ce; Matukar akwai gwagwarmaya, to da za a koma cikin kasa, sannan kuma ya ce; Gwagwarmaya tana nan da karfinta, ba ta yi rauni ba.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

Ayatullahi Makarem Shirazi Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Hadin kai Da Suka Bayar Lokacin Yakin Kwanaki 12

Ayatullah Makarem Shirazi ya jaddada cewa: An kara samun karfafan hadin kan al’umma Iran bayan wuce gona da irin ‘yan sahayoniyya da Amurka kan kasarsu

Ayatullah Nasser Makarem Shirazi, babban malamin addinin Musulunci a birnin Qum mai tsarki na kasar Iran ya jaddada cewa: An kara samun hadin kan kasa bayan yakin wuce gona da iri da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka kaddamar kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

A yayin ganawarsa da shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian a jiya Laraba a birnin Qom mai alfarma Ayatullah Makarem Shirazi ya yi ishara da yakin tunani da gwamnatin ‘yan Sahayoniyya da Amurka suka yi kan Iran yana mai cewa: Wadannan makiya sun yi zaton za su haifar da rudani ta hanyar kai wa Iran hari, amma alhamdulillahi ba wai kawai hakan ya faru ba, amma hadin kan al’ummar kasar ya kara karfafa. A wani bangare na jawabin nasa, Ayatullah Makarem Shirazi ya bayyana wasu manyan matsaloli guda uku da al’umma ke fuskanta: hauhawar farashin kayayyaki, gidajen haya, da samar da ayyukan yi ga matasa. Ya ce, “Dole ne a yi kokarin magance wadannan matsalolin, kuma in Allah idan ya yarda za a yi nasara.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Musulmi A Amurka Sun Fara Daukar Matakan Tsaro A Masallatai Saboda Makiya
  • Yawan Mutanen Da Suka Rayukansu A Rikicin Lardin Suwaida Na Kasar Siriya Ya Kai 1,400
  • Mutanen A Netherlands Suna Zaman Dirshen Saboda Gaza
  • Faransa Zata Bayyana Amincewa Da Samuwar kasar falasdinu
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jaddada Aniyar Iran Ta Ci Gaba Da Inganta Sinadarin Uranium
  • Kungiyar “Human Right Watch” Ta Yi Kira Da A Saki Tsohon Shugaban Kasar Nijar Muammad Bazoum
  • Ayatullahi Makarem Shirazi Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Hadin kai Da Suka Bayar Lokacin Yakin Kwanaki 12
  • Gwamantin Kasar Siriya Ta Rufe Hanyoyin Shiga BirninSiweida Na Kasar Saboda Ci Gaba Da Bullar Rikici
  • Iran Ta Zargi Amurka Da HKI Da Wargaza Dokokin Kasa Da Kasa Da Kuma Yarjeniyoyin Kasa Da Kasa