HausaTv:
2025-11-02@21:33:15 GMT

HKI Ta ce Ta Tsaida Yaki A Gaza Na Wani Lokaci

Published: 27th, July 2025 GMT

Majiyar sojojin HKI ta bada sanarwan cewa sun tsaida yaki na wucin gadi a gaza, don baya kungiyoyin agaji na MDD su shigar da abinci zuwa zirin gaza inda Falasdinawa suke mutuwa saboda yunwa.

Babu wata majiya ta MDD ko kuma na kungiyoyin agaji masu zaman kansu da suka tabbatar da labarin. Kuma mafi yawan kungiyayin sun bayyana cewa sai gani a kasa.

Don hki ba abar amincewa bace. Tun shekara ta 2023 ne HKI ta kara tsananta hana shigo da abinci gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka

Wani sojan Ƙasar Amurka ɗan asalin Jihar Kano, Suleiman Isah, wanda yake aiki a rundunar sojin Amurka, ya ce ba zai yaƙi da ƙasarsa ta haihuwa ba saboda yaɗa labaran ƙarya game da yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya.

Isah, wanda ya shiga rundunar sojin Amurka shekaru biyu da suka gabata, yana aiki ne da rundunar California Army National Guard, mai dakaru sama da 18,000.

Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook wanda Aminiya ta tabbatar, Isah ya mayar da martani kan jita-jitar cewa Amurka za ta ɗauki matakin yaƙi a kan Najeriya saboda zargin yi wa Kiristoci kisan gilla.

Ya bayyana cewa ba zai taɓa amfani da makami a kan mutanensa ba.

“Ba zan shiga Najeriya na kashe iyayena ba saboda ƙaryar cewa ana kashe Kiristoci,” in ji shi.

Ya ce duk da yake yana Allah-wadai da kashe-kashe da tashin hankali, bai kamata matsalar tsaro a Najeriya a danganta da wani addini ba.

“Ba zan ƙaryata batun kisan Kiristoci da Musulmai ba,” in ji shi.

“Shekau, Bello Turji, Dogo Gide da sauransu ba suna kai wa wani addini ɗaya hari ba ne kaɗai.”

Maganganun Isah na zuwa ne daidai lokacin Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar ɗaukar matakin yaƙi a kan Najeriya.

Sai dai Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa matsalar tsaro a Najeriya ba ta addini ba ce, inda ta ce matsalar na shafar Musulmai da Kiristoci baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazanar Sa Ga Nijeriya
  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A
  • Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa